Labaran Ketare
Biden da Trump Sun Yi Nasarar Lashe Zaɓen Fitar da Gwani a Michigan
Shugaban Amurka, Joe Biden da abokin karawar sa Donald Trump sun lashe zaɓen fitar da gwani na jam’iyyun su, a jihar Michigan.
Sakamakon da aka tattara daga runfunan zaɓen jam’iyyar Democrat da kuma Republican sun nuna cewa ƴan takarar biyu za su kara da juna a zaɓen shugaban ƙasar Amurka da za a yi cikin watan Nuwamban bana.
Daga alƙalumman da aka tatattara dai, masu zaɓe a jihar Michigan sun zaɓi shugaba mai ci yanzu, da kuma tsohon shugaban Amurkan a matsayin ƴan takarar su a zaɓe mai zuwa.
Sai dai kuma, shugaba Biden ya fuskanci tirjiya daga wasu ƴan jam’iyyarsa masu ƙyamar yadda ya ke goyon bayan Isra’ila a yaƙin da take a Gaza.
Masu sharhi sun ce Mr Biden ya fuskanci wannan tirjiya ne saboda akwai Amurkawa masu tsatson Larabawa masu yawan gaske a jihar Michigan, kuma dama can sun sha alwashin nuna rashin jin daɗin su ga matsayar shugaban Amurkan a kan yaƙin Gaza.
BBC
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
