Labarai
Ana Cigaba Da Ceto Mutanen Da Suka Makale Wajen Hakar Ma’adanai A Naija
Masu aikin ceto sun ceto mutane bakwai da suka makale a wani wajen hakar ma’adanai a yankin Galadima Kogo da ke karamar hukumar Shiroro ta Jihar Neja.
Ministan ma’adanai, Dele Alake ya bayyana hakan a wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai, Segun Tomori ya fitar ranar Talata a Abuja.
Ya ce an tura masu bayar da agaji zuwa wajen da lamarin ya faru, inda ya kara da cewa ana aikin ceton tare da hadin gwiwar kamfanin hakar ma’adanai.
Kamfanin dillancin labaran Nijeriya (NAN), ya ruwaito cewa kimanin mutane 30 ne suke makale cikin ramin da ake hakar ma’adanai da wani ke aiki.

Kamfanin dillancin labaran na NAN ya kara da cewa Darakta-Janar na Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA)Alhaji Abdullahi Arah ya ce lamarin ya faru ne sakamakon mamakon ruwan sama.
Ministan ya ce kokarin da gwamnatin tarayya ke yi ya nuna yadda ta himmatu wajen ganin an dakile asarar rayuka, da kuma ceto wadanda suka makale.
“Da samun labarin faruwar lamarin, sai muka tura jami’an kula da ma’adanai na tarayya (FMO) da jami’an hukumar binciken ma’adanai wajen domin ceto wadanda suka makale“.
“Tare da hadin gwiwar kamfanin hakar ma’adanai, mun ceto mutane bakwai da suka makale, ana kuma ci gaba da gudanar da aikin ceto a wajen,” in ji shi.
Ya bada tabbacin cewa gwamnatin tarayya ta kuduri aniyar yin bincike kan musabbabin afkuwar lamarin.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai16 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
