Labarai
Karamar Hukumar Kiyawa Ta Raba Harami Da Kudade Ga Mahajjata
Majalisar karamar hukumar Kiyawa ta bada gudunmawar naira dubu dari bakwai ga maniyyatan aikin hajjin bana na yankin.
Shugaban karamar hukumar, Alhaji Nasiru Ahmad ya bayyana haka lokacin da yake jawabin ban kwana ga maniyyatan a sakatariyar karamar hukumar.
Ya ce kowane maniyyaci zai karbi naira dubu ashirin, haka kuma maniyyata maza za su karbi Harami, yayin da aka rabawa maniyyata mata turamen atamfa.
A don haka, ya bukaci maniyyatan yankin su zama jakadu nagari a lokacin da suke kasa mai tsarki.
A jawabansu daban daban jami’in shiyya na hukumar jin dadin alhazai, Abdullahi Abubakar Garba da mataimakin daraktan ma’aikata na karamar hukumar Kiyawa, Alhaji Rabiu Tela sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa wannan tallafi da ya baiwa maniyyatan.
A jawabin ta na godiya a madadin maniyyata mata, Malama Maimuna Muhammad ta bada tabbacin maniyyatan za su ci gaba da yin addu’o’in neman dorewar zaman lafiya da karuwar arziki ga karamar hukumar Kiyawa da jihar Jigawa da ma kasa baki daya.
Usman Mohammed Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
