Labarai
Shugaban Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ya Yi Murabus
Shugaban hukumar leken asiri ta kasar Isra’ila, Manjo-Janar Aharon Haliva, ya yi murabus saboda harin da ba a taba ganin irinsa ba da kungiyar Hamas ta kai wa kasar.
Manjo- Janar Aharon Haliva, shi ne babban hafsan soji na farko da ya yi murabus bayan caccakar da ya fuskanta kan gagarumin harin na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.
A takardarsa ta barin aiki, Haliva ya ce ya dauki laifin kasa dakile harin da ya sa Hamas ta tsallaka katangar Iyaka da ma duk matakan tsaron Isra’ila har ta kai harin da aka kashe mutane dubu daya da dari daya da talatin da tara, ta kuma yi awon gaba da wasu darruruwa zuwa Gaza, inda ta yi garkuwa da su.
Ana ganin hakan zai bude kofa da manyan jami’an sojin kasar za su dauki laifin harin da ake ganin Hamas ta kada hantar Isra’ila fiye da kowane lokaci.
-
Labarai4 days ago
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
-
Fasaha5 days ago
Kasuwar Panteka Ta Kaduna Ta Samu Lasisin Koyar Da Sana’o’i —NBTE
-
Labarai5 days ago
Sheikh Bin Uthman Ya Jaddada Muhimmancin Rikon Amana Ga Jami’an Hukumar Alhazai
-
Labarai5 days ago
Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana
-
Labarai5 days ago
Varane zai bar Manchester United
-
Labarai3 days ago
Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai
-
Labarai5 days ago
Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar