Connect with us

Fasaha

Shirin Uwargidan Shugaban Kasa Ya Fara Aiki A Arewacin Nijeriya

Published

on

Mutane masu lalurar nakasa su 100 za su amfana da shirin gwamnatin jihar Plateau na naira dubu 100 kowanensu domin bunkasa samarda abinci.

Uwargudan shugaban kasa Sanata Olureni Tinubu ta bayyana wannan gudummuwa a wane banagre na Shirin sabonta fata da ofishinta ke gudanarwa.

Wannan. Shirin dai na sabunta fata, ofishin uwargidan shugaban kasa ne ya fito da shi domin tallafawa mata da masu lalurar nakasa da kula da ilimin mata da lafiya da aikin gona da karfafa mudu gwiwa su Iya dogaro da kansu.

Uwargidan shugaban kasar Sanata Oluremi Tinubu Kuma shugabar wannan shirin ta fada wajen kaddamar shi a yankin arewa ta tsakiya cewa, an gabatar da Shirin a kowane yanki in Banda yankin kudu maso kudu da za a gabatar Nan gaba.

Uwargidan shugaban kasar wacce ta sami wakilcin uwargidan shugaban ma’aikatan fadar Shuganan kasa kuma daraktar Shirin karfafa al’umma Mrs. Salamatu Gbajabiamila, Sanata Tinubu ta za a raba naira miliyan 10 ga mata 20 daga yankin Arewa ta tsakiya domin su ma su Sami damar gudanar akin gona don su ciyarda kansu.

Don haka Tayi kira ga wadanda zasu amfana da shirin su kashe kudaden su ta hanyar da ta dace.

A jawabinta tunda farko, uwargidan gwamnan Jihar Plateau Mrs. Helen Mutfwang wacce ta sami wakilcin kwamishiniyar ma’aikatar ilimi mai zurfi Mrs. Kachallom Gang ta bayyana mata a matsayjn kashin bayan kowace al’umma don haka tayi kira ga sauran matan gwamnonin jahohi suma su aiwatar da irin wannan Shirin a jahohinsu.

A sakonnin su daban daban, uwargidan gwamnan jihar kwara kuma shugabar Shirin ta jahohin ta tsakiya Farfesa Olufolake Abdurrazak wacce ta Sami wakilcin uwargidan shugaban majalisar wakilai Hajiya Sa’adatu da Kuma gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang dukkanin su bakinsu ya zo daya wajen godiya ga uwargidan shugaban kasa Sanata Olufemi Tinubu saboda wannan tallafin nata ga masu lalurar nakasa da ke tsakanin al’umma

Daga cikin abubuwan DA aka gabatar wajen wannan Taron shi ne gabatar da cakin kudi naira miliyan 10 ga jahohin arewa ta tsakiya da birnin Abuja da zasu amfana da shirin.

A yankin Arewa Maso Gabas Kuwa, Sanata Tinubu ta mika cek na Naira miliyan goma ga wadanda su ne matan shugabannin shiri a jihohinsu domin ci gaba da rabawa mata manoma a shirin.

Uwargidan mataimakin shugaban kasa Hajiya Nana Kashim Shettima ta wakilci uwargidan shugaban kasar, ta roki wadanda suka amfana da su kara fadada ayyukan su na noma a fannin kiwon dabbobi, kiwon kifi ko kiwon kaji domin bayar da tasu gudummawar wajen samar da abinci na gida da kasa baki daya.

Ta bayyana kwarin gwiwar cewa shirin ba wai kawai zai canza rayuwar daidaikun wadanda suka ci gajiyar shirin ba ne, har ma zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci a yankin Arewa maso Gabas.

A Arewa Maso Yamma Kuwa da aka gabatar a Birnin Kbbi, Uwargidan Shugaban kasa ta bayyana cewa shirin zai tallafa wa mata dari da arba’in a harkar noma da kudi naira dubu dari biyar kowacce kuma za a tallafa wa mutum dari daya masu bukata ta musamman da Naira dubu dari kowane.

Uwargidan kakakin majalisar wakilai Fatima Tajuddeen Abbas ta wakilce ta, ta ce shirin zai hada kai da ma’aikatar noma ta tarayya domin tabbatar da samar da abinci da kuma dorewar abinci a kasar.

Don haka ta bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudin da kayan aikin da aka ba su ta hanyar tallafa wa a samarda abinci a kasar.

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasiru Idris, a nata jawabin, ta bada nata tallafa, inda ta tallafa wa kowane mutum dari da arba’in da suka amfana da injinan fanfo mai amfani da hasken rana sannan kowane mai bukata ta musamman da kayan abinci iri-iri.

Josiah Buzum/Dauda Iliya/Abdullahi Tukur/ Shafii Wababe

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai16 hours ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai17 hours ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai18 hours ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi19 hours ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai2 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai2 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai3 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai3 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai3 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024....

Mafi Shahara