Connect with us

Fasaha

Shirin Uwargidan Shugaban Kasa Ya Fara Aiki A Arewacin Nijeriya

Published

on

Mutane masu lalurar nakasa su 100 za su amfana da shirin gwamnatin jihar Plateau na naira dubu 100 kowanensu domin bunkasa samarda abinci.

Uwargudan shugaban kasa Sanata Olureni Tinubu ta bayyana wannan gudummuwa a wane banagre na Shirin sabonta fata da ofishinta ke gudanarwa.

Wannan. Shirin dai na sabunta fata, ofishin uwargidan shugaban kasa ne ya fito da shi domin tallafawa mata da masu lalurar nakasa da kula da ilimin mata da lafiya da aikin gona da karfafa mudu gwiwa su Iya dogaro da kansu.

Uwargidan shugaban kasar Sanata Oluremi Tinubu Kuma shugabar wannan shirin ta fada wajen kaddamar shi a yankin arewa ta tsakiya cewa, an gabatar da Shirin a kowane yanki in Banda yankin kudu maso kudu da za a gabatar Nan gaba.

Uwargidan shugaban kasar wacce ta sami wakilcin uwargidan shugaban ma’aikatan fadar Shuganan kasa kuma daraktar Shirin karfafa al’umma Mrs. Salamatu Gbajabiamila, Sanata Tinubu ta za a raba naira miliyan 10 ga mata 20 daga yankin Arewa ta tsakiya domin su ma su Sami damar gudanar akin gona don su ciyarda kansu.

Don haka Tayi kira ga wadanda zasu amfana da shirin su kashe kudaden su ta hanyar da ta dace.

A jawabinta tunda farko, uwargidan gwamnan Jihar Plateau Mrs. Helen Mutfwang wacce ta sami wakilcin kwamishiniyar ma’aikatar ilimi mai zurfi Mrs. Kachallom Gang ta bayyana mata a matsayjn kashin bayan kowace al’umma don haka tayi kira ga sauran matan gwamnonin jahohi suma su aiwatar da irin wannan Shirin a jahohinsu.

A sakonnin su daban daban, uwargidan gwamnan jihar kwara kuma shugabar Shirin ta jahohin ta tsakiya Farfesa Olufolake Abdurrazak wacce ta Sami wakilcin uwargidan shugaban majalisar wakilai Hajiya Sa’adatu da Kuma gwamnan jihar Plateau Caleb Mutfwang dukkanin su bakinsu ya zo daya wajen godiya ga uwargidan shugaban kasa Sanata Olufemi Tinubu saboda wannan tallafin nata ga masu lalurar nakasa da ke tsakanin al’umma

Daga cikin abubuwan DA aka gabatar wajen wannan Taron shi ne gabatar da cakin kudi naira miliyan 10 ga jahohin arewa ta tsakiya da birnin Abuja da zasu amfana da shirin.

A yankin Arewa Maso Gabas Kuwa, Sanata Tinubu ta mika cek na Naira miliyan goma ga wadanda su ne matan shugabannin shiri a jihohinsu domin ci gaba da rabawa mata manoma a shirin.

Uwargidan mataimakin shugaban kasa Hajiya Nana Kashim Shettima ta wakilci uwargidan shugaban kasar, ta roki wadanda suka amfana da su kara fadada ayyukan su na noma a fannin kiwon dabbobi, kiwon kifi ko kiwon kaji domin bayar da tasu gudummawar wajen samar da abinci na gida da kasa baki daya.

Ta bayyana kwarin gwiwar cewa shirin ba wai kawai zai canza rayuwar daidaikun wadanda suka ci gajiyar shirin ba ne, har ma zai taimaka wajen samar da wadataccen abinci a yankin Arewa maso Gabas.

A Arewa Maso Yamma Kuwa da aka gabatar a Birnin Kbbi, Uwargidan Shugaban kasa ta bayyana cewa shirin zai tallafa wa mata dari da arba’in a harkar noma da kudi naira dubu dari biyar kowacce kuma za a tallafa wa mutum dari daya masu bukata ta musamman da Naira dubu dari kowane.

Uwargidan kakakin majalisar wakilai Fatima Tajuddeen Abbas ta wakilce ta, ta ce shirin zai hada kai da ma’aikatar noma ta tarayya domin tabbatar da samar da abinci da kuma dorewar abinci a kasar.

Don haka ta bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudin da kayan aikin da aka ba su ta hanyar tallafa wa a samarda abinci a kasar.

Uwargidan Gwamnan Jihar Kebbi, Hajiya Zainab Nasiru Idris, a nata jawabin, ta bada nata tallafa, inda ta tallafa wa kowane mutum dari da arba’in da suka amfana da injinan fanfo mai amfani da hasken rana sannan kowane mai bukata ta musamman da kayan abinci iri-iri.

Josiah Buzum/Dauda Iliya/Abdullahi Tukur/ Shafii Wababe

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara