Connect with us

Ilimi

Cibiyar Raya Albarkatun Kasa Ta Gudanar Da Taron Horaswa Na Yini 3 A Jigawa

Published

on

Majalisar dokokin jihar Jigawa ta jaddada bukatar masu ruwa da tsaki su hada kai don fadakar da jama’a da kungiyoyi kan mahimmancin fasahar kere-kere domin bunkasa sana’o’i.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ne ya bayyana hakan a lokacin bude horon kwanaki uku da cibiyar raya albarkatun kasa da ke Dutse, tare da hadin gwiwar wani kamfani suka shirya a Dutse.

Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin ya bayyana cewa, a matsayin wani sabon salo ga al’umma, ya kamata kwararru a fannin kimiyyar kere-kere su yi kokari wajen wayar da kan jama’a game da amfani da fasahar kere-kere.

Ya yi nuni da cewa, a matsayinsu na ‘yan majalisa, sun yi nazari sosai kan yadda ake amfani da fasahar kere-kere, kuma suna da ra’ayin cewa za a iya amfani da wannan fasaha a harkar noma da sauran ayyuka, kamar yadda kwararru a fannin suka bayyana.

Tun da farko, Kodinetan Cibiyar Raya Albarkatun Kasa ta Jihar Jigawa, Malam Garba Abdullahi, ya bayyana cewa an kafa cibiyar ne domin tabbatar da amfani da albarkatun da ake da su, ta hanyar amfani da ilmin halitta da fasaha wajen samar da sabbin kayayyaki, hanyoyi domin amfanin dan Adam.

Ya ce babban daraktan hukumar bincike da bunkasa fasahar kere-kere ta kasa, wanda shi ma dan asalin jihar ta Jigawa ne, ya samar da wannan cibiya, domin amfanin al’ummar jihar.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara