Labarai
Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran
Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar kai hare-hare kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila da ke yankin.
Mai magana da yawun hedikwatar, Ebrahim Zolfaghari, ya ce wannan mataki na ramuwar gayya ne inda ya zargi Amurka da Isra’ila da kai hare-hare kan gidajen fararen hula a birane daban-daban na Iran.
A cewarsa, hare-haren da ake kai wa Iran sun haddasa asarar rayukan manyan kwamandojin soja da jami’ai a lokacin rikicin.
Daga cikin waɗanda aka kashe har da Ali Khamenei, tsohon jagoran addinin Iran, wanda rahotanni suka ce an kashe shi a hare-haren hadin gwiwar Amurka da Isra’ila a ranar 28 ga Fabrairu, ranar farko ta barkewar yakin.
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
