Connect with us

Labarai

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Published

on

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su kara yin riko da abubuwan da suka koya a wannan watan na Azumi domin samun zira tare da babban rabo a duniya da Lahira.

Garkuwan Kudun Zazzau ya yi wannan kiran ne jim kadan bayan kammala taron rufe karatun wa’azin watan Ramadana na Bana da aka yi a Rigachikun lokacin da yake tattaunawa da manema labarai.

“Idan mun lura karatun da aka yi a wajen wannan rufe tafsirin na Bana a Masallacin tunawa da marigayi Shaikh Abubakar Mahmud Gumi da ke Rigachikun karkashin jagorancin Shaikh Yusuf Sambo Rigachikun duk ya ta’allaka ne ga yin biyayya ga shugabanci don haka a duk lokacin da aka ce al’umma na zaune ba tare da hadin kai da shugabanci ba lallai za a ga cewa duk karfinsu sun tarwatsa don haka a nan an koya wa al’umma sanin amfanin jagoranci su kuma shugabannin su jagoranci al’umma da adalci su kuma al’ummar su yi ma shugabannin biyayya idan hakan ta faru sai kaga al’umma na ci gaba, idan kuwa lamarin yakasance kowa na yin abin da ya ga dama ko a cikin al’umma ne idan kuwa aka kasance a cikin zaman Yan marina kowa da inda ya sa ma gaba ba tare da tunanin yin biyayya ba to, lallai wata rana za a wayi gari ta tarwatse.

“Don haka mu al’ummar Najeriya musamman mu yan arewa Musulmi muka yi amfani da wannan karantarwar in Allah yaso za a samu abin da ake nema, in kuma mun ci gaba da rayuwa a cikin irin abin da ake ciki a yanzu ba tare da shugabancin ba sai dai kawai muce wa’iyazubillahi domin ba a san abin da lamarin zai kai mu ba nan gaba.

YUSUF ZUBAIRU 

Labarai

Labarai13 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai16 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai20 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai22 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara