Connect with us

Labarai

Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna Ta Raba Abinci, Tufafi Ga Marayu, Mabukata Da Malamai

Published

on

 

Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, ta raba kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a Hayin Na’iya dake Kaduna.

An gudanar da taron ne a makarantar Ummul Muminina Hafsat Islamic Academy da ke Hayin Na’iya, Kaduna.

Hajiya Hafsat Uba Sani, wacce Hajiya Aisha Idris Maman ‘Yan Uku ta wakilta, ta jaddada bukatar ganin masu hali su tallafa wa talakawa da mabukata a cikin al’ummarsu.

“Uwargidan gwamnan ta yi imanin cewa marayu da mabukata suna bukatar soyayya, kulawa da tallafi kamar kowane yaro,” in ji ta.

“Wannan shiri ba wai kawai don samar da abinci da tufafi ba ne; yana nufin nuna musu cewa ana kaunarsu kuma ba a manta da su ba.”

“Muna karfafa gwiwar kowa da kowa da ke da hali da ya tallafa wa masu bukata,” ta kara da cewa.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban makarantar, Malam Hassan Abubakar, ya nuna matukar godiya ga uwargidan gwamnan, Hajiya Hafsat Uba Sani, saboda ci gaba da tallafinta.

Ya bayyana cewa wannan shi ne karo na biyu da take rabon kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a makarantar, baya ga hidimar da take yi wa marayu fiye da shekaru goma.

“Fiye da shekaru goma, Uwargidan gwamnan tana daukar dawainiyar marayu, tana samar musu da bukatun rayuwa ba wai abinci da tufafi kawai ba. Wannan shi ne karo na biyu tana kawo wannan tallafi zuwa makarantar mu, kuma ba za mu gaji da gode mata ba,” in ji shi.

“Muna addu’a Allah ya ba ta lafiya da kuma ci gaba, Ya sa mata albarka a cikin ayyukanta,” ya kara da cewa.

Haka nan, shugabar dalibai, Malama Fatima Abdullahi, da daya daga cikin marayun da suka amfana, sun nuna godiyarsu, suna bayyana Hajiya Hafsat a matsayin uwa gare su duka.

Sun yi addu’a Allah ya ci gaba da sa ka mata da alkhairi da kareta.

A yayin taron, an rabawa wadanda suka amfana kayan abinci, zannuwan atamfa da shadda don su more bikin Sallah cikin jin dadi da walwala.

Ci gaba da kokarin jin-kai da Hajiya Hafsat Uba Sani ke yi ya sa ta sami yabo daga jama’a, yana kara tabbatar da jajircewarta wajen inganta rayuwar mabukata a Jihar Kaduna.

 

COV: Khadija Kubau

 

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara