Labarai
Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna Ta Raba Abinci, Tufafi Ga Marayu, Mabukata Da Malamai
Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, ta raba kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a Hayin Na’iya dake Kaduna.
An gudanar da taron ne a makarantar Ummul Muminina Hafsat Islamic Academy da ke Hayin Na’iya, Kaduna.
Hajiya Hafsat Uba Sani, wacce Hajiya Aisha Idris Maman ‘Yan Uku ta wakilta, ta jaddada bukatar ganin masu hali su tallafa wa talakawa da mabukata a cikin al’ummarsu.

“Uwargidan gwamnan ta yi imanin cewa marayu da mabukata suna bukatar soyayya, kulawa da tallafi kamar kowane yaro,” in ji ta.
“Wannan shiri ba wai kawai don samar da abinci da tufafi ba ne; yana nufin nuna musu cewa ana kaunarsu kuma ba a manta da su ba.”
“Muna karfafa gwiwar kowa da kowa da ke da hali da ya tallafa wa masu bukata,” ta kara da cewa.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban makarantar, Malam Hassan Abubakar, ya nuna matukar godiya ga uwargidan gwamnan, Hajiya Hafsat Uba Sani, saboda ci gaba da tallafinta.

Ya bayyana cewa wannan shi ne karo na biyu da take rabon kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a makarantar, baya ga hidimar da take yi wa marayu fiye da shekaru goma.
“Fiye da shekaru goma, Uwargidan gwamnan tana daukar dawainiyar marayu, tana samar musu da bukatun rayuwa ba wai abinci da tufafi kawai ba. Wannan shi ne karo na biyu tana kawo wannan tallafi zuwa makarantar mu, kuma ba za mu gaji da gode mata ba,” in ji shi.
“Muna addu’a Allah ya ba ta lafiya da kuma ci gaba, Ya sa mata albarka a cikin ayyukanta,” ya kara da cewa.
Haka nan, shugabar dalibai, Malama Fatima Abdullahi, da daya daga cikin marayun da suka amfana, sun nuna godiyarsu, suna bayyana Hajiya Hafsat a matsayin uwa gare su duka.

Sun yi addu’a Allah ya ci gaba da sa ka mata da alkhairi da kareta.
A yayin taron, an rabawa wadanda suka amfana kayan abinci, zannuwan atamfa da shadda don su more bikin Sallah cikin jin dadi da walwala.
Ci gaba da kokarin jin-kai da Hajiya Hafsat Uba Sani ke yi ya sa ta sami yabo daga jama’a, yana kara tabbatar da jajircewarta wajen inganta rayuwar mabukata a Jihar Kaduna.
COV: Khadija Kubau
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
