Labarai
UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da haɗin gwiwar Gavi da ke taimakawa wajen samar da rigakafi, sun mika na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana g Gwamnatin Jihar Kano domin amfani da su a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (PHCs) guda 28 da nufin ƙarfafa rigakafin yara da kuma kula da lafiyar jama’a.
A yayin bikin mika kayayyakin ga gwamnatin jihar da Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Ƙasa (NPHCDA), Kwamishinan Lafiya na Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ya ce wannan shiri na nufin taimaka wa yaran da ba a musu rigakafi, da mata masu juna biyu da ba su da damar samun rigakafin yau da kullum da kuma wasu ayyukan kiwon lafiya.
“UNICEF tare da Gavi, ƙarƙashin shirin ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na CDS3, sun tallafa wajen saka na’urorin hasken rana a cibiyoyin PHC na kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu rigakafi a Najeriya.” In ji Dakta Labaran.
Ya ce Kano ce ta fi kowace jiha a Najeriya yawan yaran da ba a taba yi wa rigakafi ba, yana mai jaddada cewa cibiyoyin da aka saka musu wadannan na’urorin za su taka muhimmiyar rawa wajen kawar da matsalar.
Wannan aiki ya biyo bayan binciken yadda cibiyoyin lafiya a matakin farko ke aiki da wutar lantarki da UNICEF ta tallafa a shekarar 2023, wanda ya gano cibiyoyi 371 da suka cancanci a saka musu na’urorin. A wannan matakin, tare da haɗin gwiwar eHealth Systems Africa, an samar da wutar hasken rana a cibiyoyi 28 a Kano.

Tsarin zaɓen cibiyoyin ya mayar da hankali kan cibiyoyin kiwon lafiya a kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu rigakafi, tare da cire waɗanda wasu ayyuka irin su CRIBS da IMPACT suka riga suka rufe, da kuma mayar da hankali kan cibiyoyin da ba su da ingantacciyar wutar lantarki.
Dakta Labaran ya gargadi jami’an da ke kula da cibiyoyin da kada su karkatar da su don amfani na kashin kansu.
Daraktan Ƙasa na Gavi, Jessica Crawford, ta bayyana cewa wannan karamcin wani ɓangare ne na ƙoƙarin haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a Kano, inda ta ƙara da cewa Gavi za ta kashe kusan dala miliyan biyar a jihar cikin shekara biyu masu zuwa domin tallafawa manufofi da shirye-shiryen gwamnati wajen inganta lafiyar mata da yara.
Mai riƙon mukamin Shugaban Ofishin UNICEF a Kano, Michael Banda, wanda ya wakilci Shugaban Ofishin, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ya bayyana shirin a matsayin mataki na gina tsarin kiwon lafiya mai ɗorewa da adalci ga kowa.
Ya bayyana cewa samun wutar lantarki mai inganci na taimakawa wajen adana rigakafi yadda ya kamata, yin aiki a kowane lokaci, da rage dogaro da man fetur.
Taron ya samu halartar Darakta Janar na Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano, Farfesa Salisu Ibrahim, da wakilai daga WHO, Gidauniyar Gates, da sauran abokan haɗin gwiwa.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai14 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
