Connect with us

Labarai

UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano

Published

on

Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da haɗin gwiwar Gavi da ke taimakawa wajen samar da rigakafi, sun mika na’urorin samar da wutar lantarki ta hasken rana g Gwamnatin Jihar Kano domin amfani da su a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko (PHCs) guda 28 da nufin ƙarfafa rigakafin yara da kuma kula da lafiyar jama’a.

A yayin bikin mika kayayyakin ga gwamnatin jihar da Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko ta Ƙasa (NPHCDA), Kwamishinan Lafiya na Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ya ce wannan shiri na nufin taimaka wa yaran da ba a musu rigakafi, da mata masu juna biyu da ba su da damar samun rigakafin yau da kullum da kuma wasu ayyukan kiwon lafiya.

“UNICEF tare da Gavi, ƙarƙashin shirin ƙarfafa tsarin kiwon lafiya na CDS3, sun tallafa wajen saka na’urorin hasken rana a cibiyoyin PHC na kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu rigakafi a Najeriya.” In ji Dakta Labaran.

Ya ce Kano ce ta fi kowace jiha a Najeriya yawan yaran da ba a taba yi wa rigakafi ba, yana mai jaddada cewa cibiyoyin da aka saka musu wadannan na’urorin za su taka muhimmiyar rawa wajen kawar da matsalar.

Wannan aiki ya biyo bayan binciken yadda cibiyoyin lafiya a matakin farko ke aiki da wutar lantarki da UNICEF ta tallafa a shekarar 2023, wanda ya gano cibiyoyi 371 da suka cancanci a saka musu na’urorin. A wannan matakin, tare da haɗin gwiwar eHealth Systems Africa, an samar da wutar hasken rana a cibiyoyi 28 a Kano.

Tsarin zaɓen cibiyoyin ya mayar da hankali kan cibiyoyin kiwon lafiya a kananan hukumomin da ke da yawan yaran da ba a musu  rigakafi, tare da cire waɗanda wasu ayyuka irin su CRIBS da IMPACT suka riga suka rufe, da kuma mayar da hankali kan cibiyoyin da ba su da ingantacciyar wutar lantarki.

Dakta Labaran ya gargadi jami’an da ke kula da cibiyoyin da kada su karkatar da su don amfani na kashin kansu.

Daraktan Ƙasa na Gavi, Jessica Crawford, ta bayyana cewa wannan karamcin wani ɓangare ne na ƙoƙarin haɗin gwiwa don ƙarfafa tsarin kiwon lafiya a Kano, inda ta ƙara da cewa Gavi za ta kashe kusan dala miliyan biyar a jihar cikin shekara biyu masu zuwa domin tallafawa manufofi da shirye-shiryen gwamnati wajen inganta lafiyar mata da yara.

Mai riƙon mukamin Shugaban Ofishin UNICEF a Kano, Michael Banda, wanda ya wakilci Shugaban Ofishin, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ya bayyana shirin a matsayin mataki na gina tsarin kiwon lafiya mai ɗorewa da adalci ga kowa.

Ya bayyana cewa samun wutar lantarki mai inganci na taimakawa wajen adana rigakafi yadda ya kamata, yin aiki a kowane lokaci, da rage dogaro da man fetur.

Taron ya samu halartar Darakta Janar na Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano, Farfesa Salisu Ibrahim, da wakilai daga WHO, Gidauniyar Gates, da sauran abokan haɗin gwiwa.

 

Daga Khadijah Aliyu 

Labarai

Labarai14 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara