Labarai
Radio Nijeriya Ya Kai Ziyarar Ta’aziya Ga Uwargidan Shugaba Buhari
Shugabannin Hukumomin Watsa Labarai Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya ga Tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa Aisha Buhari
Shugabannin manyan hukumomin watsa labarai na ƙasa Hukumar Rediyon Najeriya (FRCN), Gidan Talabijin na Ƙasa (NTA), da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) – sun kai ziyarar ta’aziyya ga tsohuwar Uwargidan Shugaban Ƙasa, Hajiya Aisha Buhari, bisa rasuwar mijinta, tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Daraktan Kula da Yankin Arewa maso Yamma na Rediyon Najeriya, Mallam Buhari Auwalu, shi ne ya gabatar da tawagar, inda ya bayyana rasuwar tsohon shugaban ƙasar a matsayin babban rashi ga iyalinsa, Najeriya da ma duniya baki ɗaya.
Yayin ziyarar, Daraktan Sashen Injiniya na Hedikwatar Rediyon Najeriya, Injiniya Sanda Askira, ya roƙi Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta wa marigayin kuma ya saka masa da Aljannatul Firdaus.
A madadin dangin marigayin, Dujiman Adamawa, Alhaji Musa Yola, ya nuna godiya ga Daraktocin Janar da sauran tawagar bisa wannan ziyarar ta’aziyya.
Ya ce wannan alamar jajantawa da nuna ƙauna ya zama babban ƙarfafawa ga iyalan marigayin a wannan lokaci na jimami.
Tawagar ta kuma kai ziyarar ta’aziyya ga ɗan uwan tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Mamman Daura.
Daraktocin Janar sun bayyana cewa za a ci gaba da tuna tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari bisa gaskiyarsa, ƙaunarsa ga ƙasa da kuma gudunmawarsa wajen cigaban siyasa da tattalin arzikin Najeriya.
Haka kuma, sun yi addu’ar Allah ya baiwa iyalansa haƙuri da ƙarfin zuciya, tare da roƙon ‘yan Najeriya da su ci gaba da rayuwa bisa ƙa’idoji da dabi’un da marigayin ya tsaya kai da fata a kansu.
A nasa bangaren, Alhaji Mamman Daura ya nuna matuƙar godiya bisa ziyarar, yana mai bayyana ta a matsayin abin ƙarfafawa da kuma nuna haɗin kan ƙasa.

Ya gode wa shugabannin hukumomin labarai bisa addu’o’insu da kalamai masu daɗi da goyon baya da suka nuna wa iyalan Buhari a wannan lokaci na juyayi.
Cov/Adamu Yusuf
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
