Labarai
Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin Najeriya, waɗanda suka jikkata a bakin aiki, da kuma iyalan waɗanda suka rasa rayukansu yayin hidima ga ƙasa.
Shugaban ya bayyana wannan shiri ne a ranar Lahadi, a yayin da yake bikin cika shekaru 74 da haihuwarsa, domin girmama jarumtaka, sadaukarwa da hidimar da jami’an soji ke yi wa ƙasa.
Bola Ahmed Tinubu ya umarci Akanta-Janar na Tarayya da ya buɗe wani asusu na musamman domin wannan shiri, wanda zai rika bayar da tallafi ga sojojin da suka jikkata, da kuma zawarawa, mazajen da matansu suka rasu, da ’ya’yan waɗanda suka mutu yayin hidimar ƙasa.
A matsayin gudunmawar sa ta kai tsaye, shugaban ya yi alƙawarin bayar da dukkan albashinsa tun bayan hawansa mulki a matsayin jarin farko na asusun, domin nuna aniyarsa na tabbatar da cewa ba a manta da waɗanda suka sadaukar da kansu domin zaman lafiya da tsaron ƙasa ba.
Shugaban ya kuma yi kira ga gwamnonin jihohi, ’yan majalisar dokoki ta ƙasa, kamfanoni masu zaman kansu, abokansa da masu fatan alheri da su mara wa wannan shiri baya, yana mai cewa za a bayyana cikakkun bayanai game da asusun nan gaba kaɗan.
Bola Ahmed Tinubu ya jaddada cewa wannan shiri ya samo asali ne daga nauyin da ke kan ƙasa na kula da waɗanda ke sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa, da kuma iyalansu da ke ɗaukar nauyin wannan sadaukarwa, ba tare da la’akari da shirye-shiryen inshora da ake da su ba.
Ya ƙara da cewa tallafa wa jami’an soji da iyalansu ba sadaka ba ce, illa wata wajibci ce da ya kamata kowa ya cika.
Shugaban ya kuma sake jaddada kudurin gwamnatinsa na ƙarfafa jin daɗin rayuwar jami’an soji, tare da tabbatar da cewa ana girmama hidimarsu ga ƙasa ta hanyar kulawa mai ɗorewa.
Bello Wakili
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai7 days agoGwamnatin Kano ta Samar da Babura Don Inganta Yaki da Cutar Tarin Fuka a Karkara
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
