Connect with us

Labarai

Sheikh Jangebe Ya Yi Kira ga Gwamnatin Tarayya da Ta Ba da Muhimmanci ga Samar da Ayyukan Yi a 2026

Published

on

Fitaccen malamin addinin Musulunci a jihar Zamfara, Sheikh Tukur Sani Jangebe, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matsalar rashin aikin yi a matsayin babban abin da ya kamata a ba da fifiko a shekarar 2026, yana mai jaddada cewa samar wa matasa ayyukan yi na da matuƙar muhimmanci ga daidaiton tattalin arziƙi da zaman lafiya a ƙasar nan.

Sheikh Jangebe ya yi wannan kira ne yayin da yake zantawa da ’yan jarida a Gusau, babban birnin jihar Zamfara, inda ya nuna damuwarsa kan yadda adadin matasan da suka kammala karatu amma ba su da aikin yi ke ƙaruwa a faɗin ƙasar nan.

Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ƙara zage damtse wajen samar da ayyukan yi, musamman ga maza da mata masu digiri na jami’a, shaidun ƙwarewa, har ma da masu digirin digirgir (PhD) da har yanzu ba su samu aikin da zai ɗauke su ba.

A cewarsa, samar wa masu karatun jami’a ayyukan yi ya zama wajibi a koyaushe, domin hakan zai ba su damar tallafa wa kansu da iyalansu tare da bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.

Sheikh Jangebe ya kuma kalubalanci gwamnonin Arewa da su ƙara ƙoƙari wajen inganta tsaro, ilimi, kiwon lafiya, samar da hanyoyi, noma da bunƙasa kiwon dabbobi.

Ya ƙara da cewa tallafa wa ’yan kasuwa da ƙananan sana’o’i zai taimaka matuƙa wajen haɓaka tattalin arziƙi da rage talauci.

Dangane da matsalar tsaro, malamin ya roƙi Gwamnatin Tarayya, Majalisar Ƙasa, ministoci da sauran masu ruwa da tsaki da su fuskanci kalubalen rashin tsaro da cikakken muhimmanci, yana mai gargaɗin cewa zaman lafiya da ci gaba ba za su wanzu ba tare da ingantaccen tsaro ba.

A wannan fanni, ya yi kira ga dattawan ƙasa, tsofaffin manyan jami’an tsaro da sauran ’yan Nijeriya masu tasiri da su haɗa kai wajen bai wa Gwamnatin Tarayya shawarwari masu amfani, tare da buƙatar ta kare cikakken ’yancin kan Nijeriya da ƙarfi ba tare da dogaro da ƙasashen waje ba wajen magance matsalolin tsaro.

Da yake magana kan jin daɗin al’umma, Sheikh Jangebe ya shawarci gwamnatoci a faɗin Nijeriya, Arewa da Kudu, da su yi koyi da shirin kula da tsofaffi na jihar Abia.

Ya yaba wa Gwamnatin Jihar Abia ƙarƙashin Gwamna Alex Otti bisa kafa Dokar Kula da Tsofaffi ta Jihar Abia ta 2025, wadda ta tanadi tallafin kuɗi na wata-wata, kiwon lafiya kyauta da cibiyoyin kula da tsofaffi ga mutanen da suka kai shekaru 60 zuwa sama.

Ya ce idan Jihar Abia ta samu nasarar aiwatar da irin wannan tsari, to jihohin Arewa ma za su iya ɗaukar makamancin matakai domin inganta walwala da mutuncin tsofaffin al’umma.

Sheikh Jangebe ya nuna ƙwarin gwiwar cewa jihohi irin su Kano, Kaduna, Sokoto, Zamfara, Borno, Bauchi, Kebbi da sauransu na da ƙarfin aiwatar da manufofin da za su shafi jama’a kai tsaye, tare da inganta rayuwar al’ummarsu.

Malamin ya kuma yi addu’o’in sabuwar shekara, yana roƙon Allah Ya albarkaci Nijeriya da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa, tare da bayyana fata cewa shekarar 2026 za ta fi 2025 albarka, wadata da haɗin kan ƙasa.

Da yake tsokaci kan kasafin kuɗin Gwamnatin Tarayya na 2026, Sheikh Jangebe ya yaba wa ɓangaren zartarwa bisa tanadin manyan kuɗaɗe da aka yi domin inganta rayuwar al’umma ta hanyar ayyukan ci gaba a faɗin ƙasar nan, amma ya jaddada cewa aiwatarwa cikin gaskiya da riƙon amana ne mabuɗin samun nasarar da ake fata.

A ƙarshe, ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a aiwatar da ayyuka da su ji tsoron Allah, su guji cin hanci da rashawa da cin amanar jama’a, su kauce wa zalunci, tare da tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da dukiyar jama’a, yana mai cewa waɗannan ɗabi’u ne kaɗai za su rage wahalhalu da dawo da amincewar jama’a.

COV / Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara