Labarai
Sheikh Jangebe Ya Yi Kira ga Gwamnatin Tarayya da Ta Ba da Muhimmanci ga Samar da Ayyukan Yi a 2026
Fitaccen malamin addinin Musulunci a jihar Zamfara, Sheikh Tukur Sani Jangebe, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matsalar rashin aikin yi a matsayin babban abin da ya kamata a ba da fifiko a shekarar 2026, yana mai jaddada cewa samar wa matasa ayyukan yi na da matuƙar muhimmanci ga daidaiton tattalin arziƙi da zaman lafiya a ƙasar nan.
Sheikh Jangebe ya yi wannan kira ne yayin da yake zantawa da ’yan jarida a Gusau, babban birnin jihar Zamfara, inda ya nuna damuwarsa kan yadda adadin matasan da suka kammala karatu amma ba su da aikin yi ke ƙaruwa a faɗin ƙasar nan.
Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ƙara zage damtse wajen samar da ayyukan yi, musamman ga maza da mata masu digiri na jami’a, shaidun ƙwarewa, har ma da masu digirin digirgir (PhD) da har yanzu ba su samu aikin da zai ɗauke su ba.
A cewarsa, samar wa masu karatun jami’a ayyukan yi ya zama wajibi a koyaushe, domin hakan zai ba su damar tallafa wa kansu da iyalansu tare da bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.
Sheikh Jangebe ya kuma kalubalanci gwamnonin Arewa da su ƙara ƙoƙari wajen inganta tsaro, ilimi, kiwon lafiya, samar da hanyoyi, noma da bunƙasa kiwon dabbobi.
Ya ƙara da cewa tallafa wa ’yan kasuwa da ƙananan sana’o’i zai taimaka matuƙa wajen haɓaka tattalin arziƙi da rage talauci.
Dangane da matsalar tsaro, malamin ya roƙi Gwamnatin Tarayya, Majalisar Ƙasa, ministoci da sauran masu ruwa da tsaki da su fuskanci kalubalen rashin tsaro da cikakken muhimmanci, yana mai gargaɗin cewa zaman lafiya da ci gaba ba za su wanzu ba tare da ingantaccen tsaro ba.
A wannan fanni, ya yi kira ga dattawan ƙasa, tsofaffin manyan jami’an tsaro da sauran ’yan Nijeriya masu tasiri da su haɗa kai wajen bai wa Gwamnatin Tarayya shawarwari masu amfani, tare da buƙatar ta kare cikakken ’yancin kan Nijeriya da ƙarfi ba tare da dogaro da ƙasashen waje ba wajen magance matsalolin tsaro.
Da yake magana kan jin daɗin al’umma, Sheikh Jangebe ya shawarci gwamnatoci a faɗin Nijeriya, Arewa da Kudu, da su yi koyi da shirin kula da tsofaffi na jihar Abia.
Ya yaba wa Gwamnatin Jihar Abia ƙarƙashin Gwamna Alex Otti bisa kafa Dokar Kula da Tsofaffi ta Jihar Abia ta 2025, wadda ta tanadi tallafin kuɗi na wata-wata, kiwon lafiya kyauta da cibiyoyin kula da tsofaffi ga mutanen da suka kai shekaru 60 zuwa sama.
Ya ce idan Jihar Abia ta samu nasarar aiwatar da irin wannan tsari, to jihohin Arewa ma za su iya ɗaukar makamancin matakai domin inganta walwala da mutuncin tsofaffin al’umma.
Sheikh Jangebe ya nuna ƙwarin gwiwar cewa jihohi irin su Kano, Kaduna, Sokoto, Zamfara, Borno, Bauchi, Kebbi da sauransu na da ƙarfin aiwatar da manufofin da za su shafi jama’a kai tsaye, tare da inganta rayuwar al’ummarsu.
Malamin ya kuma yi addu’o’in sabuwar shekara, yana roƙon Allah Ya albarkaci Nijeriya da zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa, tare da bayyana fata cewa shekarar 2026 za ta fi 2025 albarka, wadata da haɗin kan ƙasa.
Da yake tsokaci kan kasafin kuɗin Gwamnatin Tarayya na 2026, Sheikh Jangebe ya yaba wa ɓangaren zartarwa bisa tanadin manyan kuɗaɗe da aka yi domin inganta rayuwar al’umma ta hanyar ayyukan ci gaba a faɗin ƙasar nan, amma ya jaddada cewa aiwatarwa cikin gaskiya da riƙon amana ne mabuɗin samun nasarar da ake fata.
A ƙarshe, ya yi kira ga duk masu ruwa da tsaki a aiwatar da ayyuka da su ji tsoron Allah, su guji cin hanci da rashawa da cin amanar jama’a, su kauce wa zalunci, tare da tabbatar da gaskiya da riƙon amana wajen tafiyar da dukiyar jama’a, yana mai cewa waɗannan ɗabi’u ne kaɗai za su rage wahalhalu da dawo da amincewar jama’a.
COV / Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
