Labarai
Sarkin Musulmi Ya Bukaci A Fara Duban Sabon Jinjirin Wata A Gobe Talata
Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar ya yi kira ga al’ummar Musulmin kasar nan da su fara neman ganin jinjirin watan Rajab a gobe Talata 31 ga watan Disamban 2024, daidai da kalandar Musulunci 29 ga watan Jumada Thani Hijira ta 1446.
A wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addinin musulunci na jihar Sokoto Farfesa Sambo Wali Junaidu, kuma Wazirin Sokoto, ya ce idan an gani sai a sanar ga gunduma ko kauye mafi kusa domin sanar da Sarkin Musulmi.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, duban wata yana fayyace kalandar Musulunci a cikin shekara guda, wanda hakan ya sa ganin watan Ramadan ya fi karbuwa ga al’ummar Musulmin kasar baki daya.
Daga Nasiru Malali
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
