Connect with us

Labarai

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Yi Wawan Kamu

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama wasu mutane 19 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane da sauran laifukan da suka shafi ‘yan fashi.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Sufurtandan Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.

 

Ya ce an samu nasarar kame mutanen ne ta hanyar sintiri da kuma tattara bayanan sirri.

 

Kiyawa ya bayyana cewa, kayyakin da aka gano sun hada da bindigogi kirar AK-47 guda biyu, bindigarsamfurin harbi ka ruga daya, bindiga kirar famfo guda daya, alburusai 26, harsashi masu rai guda 17, motoci guda biyu, raguna 16, da sauran muggan makamai da na fasa gidaje.

 

“Ana ci gaba da bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.”

 

Ya yi nuni da cewa Kwamishinan ‘yan sanda, CP Mohammed Usaini Gumel, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da yin aiki tukuru domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma gurfanar da masu aikata laifuka a gaban kuliya.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara