Labarai
Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki su kara kaimi wajen tallafa wa mata da ’yan mata a fadin jihar.
Ta bayyana hakan ne yayin bikin Ranar Mata ta Duniya, inda ta ce bikin na tunatar da muhimmiyar rawar da mata ke takawa wajen gina iyali, al’umma da kuma ci gaban kasa.
Kwamishinar ta jaddada kudurin ma’aikatar wajen inganta daidaito tsakanin maza da mata, kare hakkin mata da yara, da kuma samar da damar da za ta ba mata damar cimma burinsu.
Ta kuma yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf kan goyon bayan manufofi da shirye-shiryen da ke karfafa mata da kuma kula da marasa karfi a Kano.
A karshe, ta bukaci iyalai da kungiyoyi su kara tallafa wa shirye-shiryen ilimi, kasuwanci da jagoranci ga mata, domin gina al’umma mai adalci inda kowa zai samu dama ba tare da wariya ba.
Khadijah Aliyu/Kano
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
