Connect with us

Labarai

Najeriya Ta Shirya Aiwatarda Yarjejeniyar Fahimta Tsakanin NTA, FRCN Da China Media Group

Published

on

 

Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya jaddada kudurin Najeriya na aiwatar da cikakken yarjejeniyar biyu da aka kulla tsakanin China Media Group da manyan gidajen watsa labarai na gwamnati a Najeriya – Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN) a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a Beijing.

 

Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi Jakadan Sin a Najeriya, Mista Yu Dunhai, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa a yau alhamis. Ya ce, wadannan yarjejeniyoyi sun ƙudiri aniyar ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin watsa labarai da sadarwa, domin inganta dangantakar Najeriya da Sin.

 

Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun shafi musayar bayanai da fasahar zamani, wanda hakan zai inganta ƙwarewar gidajen watsa labaran Najeriya tare da ɗaukaka su zuwa matakin da ya dace da kyawawan ƙa’idojin duniya.

 

“Najeriya da Sin a matakin hulɗar diflomasiyya suna da ƙawance mai ƙarfi matuka. Wannan ya haifar da sanya hannu kan yarjejeniyar fahimta guda 10 a Beijing, kuma guda biyu daga cikinsu suna da nasaba da wannan ma’aikata. Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) ita ce cibiyar talabijin mafi girma a duk faɗin Afirka, tana da tashoshi sama da 100 da ke rufe dukkan yankuna tare da isa ga mutane sama da miliyan 200. Yana da matuƙar muhimmanci, kuma abin da NTA ke son cimmawa ta hanyar wannan haɗin gwiwa da Sin shi ne musayar labarai, fasaha, da bayanai wanda zai amfanar da ƙasashen biyu. Haka kuma, muna da irin wannan yarjejeniya da ɗaya daga cikin manyan gidajen rediyo a Afirka, wato Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN). Wadannan yarjejeniyoyi sun riga sun kammala, kuma Najeriya tana da niyyar cika nata ɓangaren,” in ji shi.

 

Ministan ya ce, bayar da sahihin bayani da labarai na gaskiya zai ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashe, don haka ya nemi haɗin gwiwa da Sin wajen yaƙi da labaran ƙarya, ɓata bayani da yada bayanai na bogi.

 

“Yada labaran ƙarya ƙalubale ne ga duniya baki ɗaya. Mun san cewa Sin tana ɗaukar wannan batu da muhimmanci sosai, haka kuma mu ma a Najeriya muna ɗaukar hakan da muhimmanci. Ba matsala ba ce da ke shafar Najeriya da Sin kaɗai; matsala ce ta duniya baki ɗaya, kuma muna son yin aiki tare da Sin don yaƙi da labaran ƙarya tare da inganta watsa labarai masu amfani da za su taimaka wajen bunƙasa al’umma,” in ji shi.

 

Idris ya bayyana wa Jakadan cewa, Najeriya na da ‘yancin watsa labarai a matsayin wani muhimmin bangare na manufofin gwamnatin Tinubu don ƙarfafa dimokuradiyya ta hanyar bayar da ingantattun bayanai.

 

“Kafafen watsa labarai a nan suna da ’yanci sosai. Tabbas, akwai wasu matsaloli a lokaci zuwa lokaci, wanda koyaushe muna aiki a kansu don ingantawa. Najeriya na da babbar ’yancin watsa labarai, kuma muna so mu ci gaba da hakan,” in ji shi.

 

Ministan ya kuma bukaci kamfanonin Sin su yi amfani da sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa domin zuba jari a tattalin arzikin Najeriya.

 

A nasa jawabin, Jakada Dunhai ya ce a matsayinsa na sabon jakadan Sin a Najeriya, zai yi duk mai yiwuwa don ƙara ƙarfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.

 

Ya nuna goyon bayansa ga shirin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu, wanda ke da nufin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa don samar da ci gaba mai dorewa.

 

“A matsayina na sabon jakada, ina ganin kaina a matsayin mai sa’a saboda na zo ne a lokacin da Najeriya ke karkashin jagorancin Shugaba Tinubu, wanda ke da niyyar gina ƙasa mai ƙarfi. Haka nan, a karkashin jagorancin Shugaba Xi Jinping, Sin tana kan tafarkin sabunta ƙasa ta hanyar tsarin zamani na Sin,” in ji shi.

 

Jakadan ya tunatar da cewa a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a Beijing, Shugabannin kasashen biyu, Xi Jinping da Tinubu, sun amince da ɗaukaka dangantakar kasashen su zuwa babbar kawance ta fuskar diflomasiyya, wanda hakan zai buɗe sabon babi a dangantakar su.

 

Ya ce yana sa ran ganin yadda za a aiwatar da yarjejeniyoyin fahimta da aka kulla tsakanin NTA, FRCN da China Media Group, domin kafafen yada labarai suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen gina al’umma.

 

Jakadan ya bayyana jin daɗinsa cewa kafafen watsa labarai a Najeriya suna daidaito, gaskiya da adalci a labaran da suke watsawa, domin suna ƙoƙarin gabatar da cikakken bayani kan abubuwan da ke faruwa ga ‘yan Najeriya.

 

A bangaren zuba jari, Jakadan ya ce Shugaba Xi Jinping ya alkawarta dala biliyan 50 domin zuba jari a Afirka a cikin shekaru uku masu zuwa, a matsayin ci gaba ga yarjejeniyoyin fahimta guda goma da aka rattaba hannu a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan.

Cov/Adamu Yusuf

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara