Connect with us

Kasuwanci

Najeriya Da Jamhuriyar Benin Za Su Karfafa Zamantakewa Da Tattalin Arziki

Published

on

 

 

 

Ministocin harkokin wajen Najeriya, Alhaji Yusuf Tuggar da na Jamhuriyar Benin, Olushegun Adjadi Bakaru, sun gudanar da wani taro a ranar Talata, da nufin inganta harkokin kasuwanci tsakanin kasashen biyu, a mashigin Segbana da ke Jamhuriyar Benin.

 

Taron na tara ya kuma yi nufin dawo da mashigar tsakanin Tsamiya a Najeriya da Anguwar Sule Wara a jamhuriyar Benin zuwa rayuwa ta hanyar raya ababen more rayuwa bisa sabon fatan da shugaba Tinubu ya yi.

 

Ministan harkokin wajen Najeriya, ya ce taron ya samo asali ne bisa umarnin shugaba Bola Tinubu da shugaban kasar, Patrice Talon na Jamhuriyar Benin, na karfafa huldar zamantakewa da tattalin arziki tare da fadada kasuwanci tsakanin ‘yan kasashen biyu.

 

Ya ce, an samu ci gaba wajen karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen yammacin Afirka a dandalin.

 

Shugaban hukumar kwastam na Najeriya Bashir Adewale-Adeniyi, ya ce taron na da nufin ciyar da harkokin yankin gaba tsakanin kasashen biyu da shugabannin kasashen biyu suka riga suka kirkiro.

 

Ya bayyana cewa, a cikin watanni shida da suka gabata, Hukumar Kwastam ta Najeriya tana aiki tare da Hukumar Kwastam ta Jamhuriyar Benin, wajen kara kusantar da tattalin arzikin kasashen biyu, ta hanyar tsallakawa kan iyaka cikin sauki tare da dawo da martabar kan iyakar Tsamiya da Anguwar Sule. Wara.

 

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya godewa shugabannin kasashen biyu kan yadda suka farfado da harkokin kasuwanci da safarar kayayyaki zuwa wurare daban-daban na kasashen biyu.

 

Gwamnan ya jaddada cewa, jihar ta ci gaba da kyautata makwabtaka da jamhuriyar Benin kan harkokin tattalin arziki da mu’amalar al’umma a matsayin masu amfani a kan iyaka.

 

Romuald Wadagni, Babban Ministan Ma’aikatar Tattalin Arziki, Kudi da Hadin Gwiwa ta Jamhuriyar Benin da Mrs Adidjatou Hassan, Babban Darakta na Hukumar Kwastam ta Benin, Gwamnonin Jamhuriyar Benin da shugabannin hukumomin tsaro na jihar Kebbi sun halarci taron.

 

COV/ABDULLAHI TUKUR/Wababe

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara