Kasuwanci
Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu ya saba wa sashe na 11,12 da 13 na dokar KNUPDA za a gurfanar da shi a gaban kuliya.
A cewarsa, gargadin ya zama wajibi ganin yadda ake samun karuwar gine-gine ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba.
Manajan daraktan ya bukaci jama’a da su samu takardar izinin gini daga KNUPDA kafin su fara kowane irin gini.
Architect Ibrahim ya yi nuni da cewa gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta saukaka hanyoyin samun takardar izinin gini a jihar.
“Kwanan nan an samarda wata na’ura da za ta gaggauta ba jama’a takardar izinin gini ba kamar da a da sai an dauki watanni kafin a kammala aikin.”
Sai dai ya jaddada cewa masu neman izinin gini su kuma gabatar da zane kafin zuwa neman iznin don kwaucewa rugujewar gini a nan gaba.
Manajan daraktan ya lissafo jerin matakan da KNUPDA ta dauka don tabbatar da cikakken bin al’umma.
Ya bayyana abin takaicin da ya faru a baya-bayan nan a matsayin sakaci domin tun da farko KNUPDA ta ba su takardar su dakatar da aikin ta daya da ta biyu kafin ginin ya ruguje.
Architect Yakubu Adamu ya kuma bayyana cewa an gudanar da tarurruka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro domin gano wanda ya gina shi tare da gurfanar da shi.
Architet Ibrahim ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rigamu gidan gaskiya tare da addu’ar Allah ya wadanda suka sami rauni lafiya.
KHADIJAH ALIYU/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
