Connect with us

Kasuwanci

Mun Aika Musu Takardun Gargadi Kafin Ginin Ya Rushe – KANUPDA

Published

on

 

Manajan Daraktan Hukumar Tsare-tsare da Ci gaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), Architect Ibrahim Yakub Adamu ya yi gargadin cewa duk wanda aka samu ya saba wa sashe na 11,12 da 13 na dokar KNUPDA za a gurfanar da shi a gaban kuliya.

 

 

A cewarsa, gargadin ya zama wajibi ganin yadda ake samun karuwar gine-gine ba tare da bin ka’idojin da suka dace ba.

 

 

Manajan daraktan ya bukaci jama’a da su samu takardar izinin gini daga KNUPDA kafin su fara kowane irin gini.

 

 

Architect Ibrahim ya yi nuni da cewa gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta saukaka hanyoyin samun takardar izinin gini a jihar.

 

 

“Kwanan nan an samarda wata na’ura da za ta gaggauta ba jama’a takardar izinin gini ba kamar da a da sai an dauki watanni kafin a kammala aikin.”

 

 

Sai dai ya jaddada cewa masu neman izinin gini su kuma gabatar da zane kafin zuwa neman iznin don kwaucewa rugujewar gini a nan gaba.

 

Manajan daraktan ya lissafo jerin matakan da KNUPDA ta dauka don tabbatar da cikakken bin al’umma.

 

 

Ya bayyana abin takaicin da ya faru a baya-bayan nan a matsayin sakaci domin tun da farko KNUPDA ta ba su takardar su dakatar da aikin ta daya da ta biyu kafin ginin ya ruguje.

 

 

 

Architect Yakubu Adamu ya kuma bayyana cewa an gudanar da tarurruka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro domin gano wanda ya gina shi tare da gurfanar da shi.

 

 

Architet Ibrahim ya mika ta’aziyya ga iyalan wadanda suka rigamu gidan gaskiya tare da addu’ar Allah ya wadanda suka sami rauni lafiya.

 

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara