Connect with us

Labarai

Manyan Attajiran Duniya Sun Halarci Bikin Auren Dan Wani Attajiri A Indiya

Published

on

Wasu daga cikin manyan masu fada a ji a duniya sun isa jihar Gujarat ta kasar Indiya domin halartar bikin auren mutum mafi dukiya a nahiyar Asiya.

 

Daga cikin bakin akwai shugaban facebook Mark Zuckerberg da shahararriyar mawakiya Rihanna da tsohon wanda ya fi kowa arziki a duniya Bill Gates.

 

Dukkanin su sun halarci walimar da Mukesh Ambani, shugaban rukunin kamfanonin Reliance Industries, kuma attajiri mafi dukiya a nahiyar Asiya ya shirya domin murnan bikin auren dan shi.

 

Matashi Anant Ambani, mai shekara 28 a duniya zai auri masoyiyarsa Radhika Merchant a cikin watan Yuli.

Shahararrun ‘yan wasan fina finan  Indiya, Shah Rukh Khan da Amitabh Bachchan na daga cikin wadanda suka halarci walimar ta kwana uku wadda ta gudana a birnin Jamnagar.

 

Yanzu haka Mukesh Ambani, mai shekara 66 a duniya shi ne mutum na 10 a jerin mutane mafiya kudi a duniya, inda dukiyarsa ta kai dalar Amurka biliyan 115, kamar yadda mujallar Forbes ta bayyana.

 

Mahaifin Mukeh Ambani ne ya kafa rukunin kamfanin Reliance Industries a shekarar 1966, wanda katafaren rukunin kamfanoni ne da ya kunshi hadawa da sayar da kaya daban-daban sai kuma harkar hada-hadar kudi da na sadarwa.

 

Anant Ambani shi ne dan’auta a cikin ‘yayan mahaifin nasa uku, wadanda dukkanin su suke cikin manyan shugabannin rukunin kamfanonin na Reliance Industries.

Matashin na aiki a bangaren kasuwancin makamashi na rukunin kamfanonin kuma yana cikin shugabannin da ke tafiyar da lamurran gidauniyar rukunin kamfanonin.

 

Wannan kasaitacciyar walimar aure ta ji da gani daya ce daga cikin irin su da iyalan na Ambani suka yi kaurin suna wajen shiryawa.

A shekarar 2018, shahararriyar mawakiyar Amurka, Beyonce na daga cikin wadanda suka cashe a walimar daurin auren ‘yar Mista Ambani, Isha Ambani, wanda aka yi a birnin Udaipur. Tsofaffin sakatarorin harkokin waje na Amurka Hillary Clinton da John Kerry na daga cikin wadanda suka halarci walimar ta wancan lokaci.

 

Wani rahoto na kafar yada labaru ta Bloomberg a wancan lokaci ya kiyasta cewa an kashe kudi dalar Amurka miliyan 100 a lokacin bikin – sai dai wani ‘na kusa da iyalin Ambani’ ya musanta batun, inda ya ce kudin da aka kashe bai wuce dala miliyan 15 ba.

 

Walimar ta wannan karo ta fara ne daga farkon wannan mako, inda iyalin na Ambani suka raba abinci ga al’ummar garin Jamnagar.

Sauran bakin da aka gani wurin taron sun hada da maidakin tsohon shugaban Amurka, Ivanka Trump, da tsoffin firaministocin Canada da Autralia, wato Stephen Harper da Kevin Rudd.

 

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara