Kasuwanci
Kungiyar Musulmai Ta Bada Gudunmawar Rijiyar Burtsatse Ga Sakatariyar CAN
A kokarin da ake na samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinin Kirista da Musulmi a jihar Neja, kungiyar ilimin addinin Musulunci ta bayar da tallafin rijiyar burtsatse ga kungiyar Kiristoci ta Najeriya CAN.
Da yake jawabi a wajen kaddamar da bikin, Darakta Janar na Hukumar, Alhaji Arzika Abubakar Rimau ya ce IET ta yanke shawarar bayar da tallafin rijiyoyin burtsatse ne domin ta taimaka wajen farfado da dadaddiyar dangantakarsu.
“Samar da rijiyar burtsatse ga CAN na daga cikin kudurinmu na karfafa hadin kan addinai a jihar Neja”.
Rimau ya ce wannan karimcin na nuna dawwamammiyar gadon marigayi Sheikh Ahmed Lemu, wanda ya jajirce wajen hadin gwiwa tsakanin addinai tare da kulla alaka ta kut-da-kut da Malaman addinin Kirista kamar marigayi Father O’Connell, babban mai bayar da gudunmawa wajen ci gaban ilimi a jihar.
Yayin da yake nuna godiya a madadin al’ummar Kirista, Shugaban kungiyar CAN reshen Jihar Neja, Rabaran Bulus Dauwa Yohanna, ya bayyana matakin na IET a matsayin wata alama ta hadin kai, wanda ke karfafa hadin gwiwa tsakanin mabiya addinai biyu domin samun ci gaban al’umma.
Shima da yake nasa jawabin, Daraktan Sashen Hulda da Jama’a, Alhaji Ibrahim Yahaya ya yabawa Victoria Ndagi, wata Kirista mai kishin kasa, bisa yadda ta ja hankalin kungiyar kan bukatun ruwa na sakatariyar CAN da ke Minna babban birnin jihar Neja.
A matsayin wani ɓangare na taron, IET ta ba da lambar yabo ga Victoria Ndagi saboda rawar da ta taka wajen inganta haɗin gwiwa tsakanin addinai da haɓaka ci gaban al’umma.
An bayyana ta a matsayin wata gada tsakanin addinai, tare da lura da cewa shawarar da ta bayar ya sa IET ta fadada ayyukan jin kai ga sauran al’ummomin Kirista, saboda lambar yabo da aka ba ta ta dace sosai.
ALIYU LAWAL/Minna
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
