Connect with us

Labarai

Jihar Bauchi Zata Tarbi Taron Karrama Sir Ahmadu Bello Karo Na 11

Published

on

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za a gudanar da taron Karrama Sir Ahmadu Bello karo na 11 a ranar Asabar, 22 ga Fabrairun 2025, a Bauchi.

 

 

Wannan taron, wanda ke tunawa da rayuwa da gado na Sir Ahmadu Bello KBE, Sardaunan Sokoto da Firaministan tsohuwar Yankin Arewa, zai hada da jerin tattaunawa da ayyukan da zasu mayar da hankali wajen magance kalubalen tattalin arzikin yankin.

 

 

Taken taron na bana, “Alherin Duniya: Sauyw Albarkatun Halitta na Arewa zuwa Cigaba Mai Dorewa”, na zuwa ne a lokacin da ake fuskantar karin damuwa kan talauci da rashin aikin yi da rashin ci gaba duk da kasancewar Arewa na da yalwar albarkatun halitta.

 

 

Za a tattauna yadda yankin zai iya amfani da gonakin noma da ma’adinai da albarkatun ruwa wajen samun ci gaban tattalin arzikin da zai dore.

 

 

Wannan taron na tsawon mako guda zai hada da horo na kwarewar zamantakewa ga matasa a Jihar Bauchi da gabatar da tallafin karatu ga dalibai ‘yan asalin jihohin Arewa a makarantu na gaba da sakandire da kuma ba da kyaututtuka ga mutanen da suka cancanta a fannonin al’umma.

 

 

Tsohon Daraktan Gudanarwa na Bankin Duniya, Dr. Mansur Mukhtar OFR, zai gabatar da jawabi, yayin da His Excellency Senator George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance matsayin baƙo na musamman.

 

His Excellency Alh. Muhammadu Inuwa Yahaya CON, Gwamnan Jihar Gombe ne wanda zai jagoranci taron, tare da Gwamnan Jihar Bauchi, His Excellency Sen. Bala Mohammed CON, a matsayin babban mai masaukin baki.

 

 

Ana sa ran manyan baki a wurin taron su hada da gwamnonin jihohi da ‘yan majalisar dokoki da ministoci da sauran manyan masu ruwa da tsaki, wanda ke nufin haɓaka tattaunawa mai ma’ana da dabaru masu amfani domin bude damar ci gaban tattalin arzikin Arewa.

 

Gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello tana ci gaba da aikinta na inganta ilimi da cigaban ɗan adam, da cigaban tattalin arziki a Arewa, a cikin girmamawa da gado na marigayi Sardauna.

 

Daraktan gidauniyar, Engr. Dr. Abubakar Gambo Umar, ya bayyana farin cikinsa dangane da wannan taron, yana mai jaddada muhimmancin albarkatun halitta na Arewa wajen tsara makomar yankin.

 

“Yankin Arewa na da yalwar albarkatun halitta da noma da ma’adinai da ruwa wanda zai iya zama babban dama don haɓaka ci gaban dake dorewa,” in ji shi.

 

“Amma wannan damar za a iya cimma ta ne kawai idan muka ɗauki hanyar gudanarwa ta haɗin gwiwa da cikakken tsarin kula da albarkatu, domin tabbatar da cewa ci gaban yana faɗaɗa ga dukkanin masu ruwa da tsaki,” ya ƙara da cewa.

 

Dr. Umar ya kuma bayyana muhimmancin taron Karrama Sir Ahmadu Bello a matsayin dandalin tattaunawa a kan waɗannan kalubale.

 

Ya kara da cewa, “Wannan jerin taron yana cikin muhimmancin gidauniyar tunawa da Sir Ahmadu Bello na ƙarfafa tattaunawa mai ma’ana a kan shugabanci da cigaba mai dorewa da haɓaka tattalin arziki.

 

 

Ya ce, “yana da muhimmanci mu haɗa muryoyi daban-daban daga gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu, da ƙungiyoyin farar hula don ƙirƙirar dabaru masu amfani wajen ci gaban yankin.”

 

 

Khadija Kubau

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara