Labarai
Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Ta Yi Kira Ga Hadin Kai Da Adalci A Ramadan
Yayin da al’ummar Musulmai a Najeriya da duniya ke fara azumin watan Ramadan, Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta aike da sakon fatan alheri, tana kira da a yi amfani da wannan lokaci mai daraja wajen sabunta zukata da nuna tausayi da karfafa hadin kai a kasa.
A cikin wata sanarwa da Daraktan Janar na gidauniyar, Abubakar Gambo Umar ya sanya wa hannu, ta jaddada bukatar kyautata dabi’u da wanzar da zaman lafiya da adalci a kasuwanci a lokacin azumi.
Gidauniyar ta yi kira ga malaman addini da su ci gaba da yada sakonnin tsoron Allah da hakuri da kaunar juna, domin karfafa darussan Ramadan na sabunta imani da hadin kan al’umma.
Hakazalika, gidauniyar ta gargadi ’yan kasuwa da dillalai da su guji tsawwala farashi da cutar da mabukata, tana mai cewa Ramadan lokaci ne na tausayi da taimakon juna, ba wahala da neman riba ta haram ba.
“Yayin da muke tsarkake kanmu ta hanyar azumi da ibada, mu kuma daga murya cikin addu’a don hadin kai, zaman lafiya, da ci gaban ƙasarmu ƙaunatacciya. Allah Ya baiwa shugabanninmu shiriya, Ya kuma ba ƙasarmu ƙarfin da za ta shawo kan ƙalubalen da take fuskanta. in ji sanarwar”.
Gidauniyar ta jaddada kudirinta na karfafa zaman lafiya da adalci da daidaito a cikin al’umma, tare da kira ga ’yan Najeriya da su rungumi kyawawan halaye na Ramadan—imani, hakuri da karamci.
A karshe, gidauniyar ta yi fatan Allah Ya albarkaci kowa da zaman lafiya da rahama a wannan wata mai alfarma.
Rel: Khadija Kubau
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Maniyyatan Jihar Jigawa Ya Tashi Zuwa Kasar Saudiyya
-
Labarai2 days agoJihar Jigawa Ta Kammala Jigilar Alhazai Zuwa Kasa Mai Tsarki
-
Labarai4 days agoRukunin Farko na Alhazan Jihar Kebbi ya Isa Kasa Mai Tsarki
-
Kasuwanci2 days agoBOA da Majalisar Wakilai za su Samar da Injinan Noma a Dukkan Mazabu
-
Labarai5 days agoKashim Shettima Ya Kaddamar da Jirgin Farko na Maniyyatan Najeriya
-
Labarai2 days agoGwamna Bago Ya Umurci SEMA Ta Gaggawata Kai Tallafi ga Wadanda Iftila’in Guguwa ya Shafa a Mokwa da Bida
-
Ilimi2 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yaba wa Ministar Harkokin Mata Kan Inganta Rayuwar Al’umma
-
Labarai4 days agoGwamnan Jigawa Ya Bukaci Alhazai Su Yi Addu’ar Zaman Lafiya da Ci Gaban Najeriya
