Connect with us

Ilimi

Jami’ar Bayero Ta Kori Dalibai 171 Bisa Gabatar da Takardun Bogi

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta amince da korar dalibai 171 bisa laifin gabatar da takardun shigar jami’a na bogi.

An yanke wannan hukunci ne a yayin taron majalisar jami’ar karo na 433, bayan rahoton kwamitin majalisar kan matsalolin rashin sahihancin takardun shiga jami’ar.

A cewar wata sanarwa da jami’ar ta fitar a cikin mujallarta ta mako-mako, an gano cewa daliban da abin ya shafa sun gabatar da takardun bogi yayin neman gurbin karatu, wanda ya saba wa dokokin jami’ar.

Jami’ar ta bayyana cewa wannan laifi ya saba wa Sashe na 20.7, rukuni na A (vii) na dokokin jarabawa da harkokin ilimi, wanda ke tanadin hukuncin kora ga irin wannan laifi.

BUK ta kara da cewa daliban da abin ya shafa sun fito ne daga sassa da matakai daban-daban, tare da jaddada cewa matakin na daga cikin kokarin tsaftace harkar karatu da kuma kare martabar jami’ar.

A wani bangare kuma, majalisar ta amince da korar Yusuf Muhammad Sani, dalibi a sashen Injiniyan Gine-gine, bisa zargin hannu a dukan masu sanya ido a jarabawa.

Jami’ar ta ce lamarin ya kawo tsaiko a gudanar da jarabawar tare da karya dokokin ladabtar da dalibai.

Hukumar jami’ar ta sake jaddada kudurinta na tabbatar da gaskiya da nagarta a harkokin ilimi, tare da gargadin cewa duk wanda ya karya dokokinta zai fuskanci tsattsauran hukunci.

Labarai

Ilimi13 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara