Labarai
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano Ta Karɓi Ƙorafe-ƙorafe 12,446 a Shekarar 2025
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta bayyana cewa ta karɓi jimillar ƙorafe-ƙorafe 12,446 daga watan Janairu zuwa Disamba na shekarar 2025.
Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar, Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar, ne ya bayyana hakan yayin da yake yi wa ’yan jarida bayani a Kano.
A cewarsa, daga cikin adadin ƙorafe-ƙorafen da aka karɓa, shari’o’i 1,908 an sasanta su cikin lumana, yayin da 4,246 aka miƙa su gaban kotuna domin ɗaukar matakin doka.
Sheikh Mujahid ya bayyana cewa Hukumar Hisbah na ba da fifiko ga warware rikice-rikice ta hanyar sulhu (Alternative Dispute Resolution – ADR), musamman a lamuran zamantakewa da na iyali, domin ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a cikin al’umma.
Da yake magana kan matsalar kin ɗaukar nauyin iyali, Mataimakin Babban Kwamandan ya bayyana cewa an samu kudade har naira ₦145,406,409 da aka karɓo tare da biya domin ciyar da iyalai, ta hanyar sa hannun Hukumar Hisbah ta Jihar Kano a lokacin da ake bitar.
Ya ƙara da cewa hukumar ta gudanar da manyan ayyuka guda tara a faɗin jihar, inda ta kama mutane 132 da ake zargi, a cikin ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano.
Sheikh Mujahid ya kuma bayyana cewa bayanan da ke ofishin Hisbah sun nuna cewa mutane 93,231, maza da mata, sun ziyarci hukumar tsakanin Janairu da Disamba na shekarar 2025.
Ya shawarci al’ummar jihar da su ci gaba da rayuwa cikin zaman lafiya da jituwa, tare da ƙarfafa jama’a da su rika kai rahoton duk wani mutum ko aiki da ake zargi ga hukumomin da suka dace.
A ƙarshe, Mataimakin Babban Kwamandan ya jaddada ƙudurin Hukumar Hisbah na ci gaba da aiki ba dare ba rana domin tabbatar da cewa Jihar Kano ta kasance ba tare da munanan ɗabi’u na zamantakewa ba.
Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
