Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Farfado da Cibiyoyin Kiwon Dabbobi a Gumel, Birniwa da Kazaure

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta ware sama da naira biliyan 17 domin bunƙasa harkar kiwo a faɗin jihar.

Kwamishinan Harkokin Kiwon Dabbobi na jihar, Farfesa Abdulrahman Salim ne ya bayyana hakan ga manema labarai bayan kare kasafin kuɗin da ma’aikatarsa ta gabatar na shekarar  2026 a gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa mai kula da harkokin noma, a Dutse.

Farfesa Abdulrahman Salim ya ce za a yi amfani da kuɗaɗen wajen aiwatar da manyan ayyuka daban-daban da suka shafi bunƙasa kiwo a shekarar 2026.

Ya ƙara da cewa ma’aikatar ta shirya kafa wuraren kiwo (ranches) a sassan jihar, inda makiyaya da sauran masu kiwon dabbobi za su zauna.

A cewarsa, a waɗannan wuraren da za a ware domin kiwo, makiyaya za su samu ingantaccen abincin dabbobi, makarantu masu kyau ga ’ya’yansu, cibiyoyin lafiya, asibitocin dabbobi, kasuwanni, wutar lantarki da ruwan sha.

Farfesa Salim ya ce hakan zai taimaka wa ma’aikatar wajen rage yawan rikice-rikicen da ke faruwa tsakanin manoma da makiyaya a jihar.

Kwamishinan ya ƙara da cewa za a kuma yi amfani da kuɗin wajen kafa asibitocin dabbobi a dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar, da asibitocin dabbobi na shiyyoyi guda bakwai, tare da babban asibitin dabbobi na tsakiya da zai zama cibiyar tura marasa lafiya (referral centre).

Ya ce duk da suna da ƙwararrun likitocin dabbobi, akwai buƙatar horaswa da sake horas da ma’aikatan matsakaici da na ƙananan matakai.

Haka kuma ya bayyana cewa ma’aikatar ta shirya farfaɗo da cibiyoyin kiwon dabbobi guda uku da ke Gumel, Birniwa da ƙaramar hukumar Kazaure, inda ya ce tuni aka fara aiki a wasu daga cikin cibiyoyin.

Farfesa Salim ya ƙara da cewa za a fara ne da kafa wuraren kiwo guda uku a matsayin gwaji, tare da ƙanana da za a danganta da sarrafa kayan madara ko kayan kiwon dabbobi na makiyaya.

Ya ce ma’aikatar na da ayyuka masu yawa a fannin sarrafa nama, inda aka raba su kashi biyu. Na farko shi ne ayyukan mazabun ’yan majalisar dokoki da suka kai kimanin naira miliyan 355, waɗanda suka haɗa da gina wuraren yanka dabbobi da manyan gidajen yanka.

 

 

 

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara