Labarai
Gwamnati Ta Tabbatarda Kungiyoyin Hadaka A Matsayin Ginshikin Ci gaban Al’umma
Gwamnatin Tarayya ta ce ta gano irin muhimmiyar gudunmuwar da kungiyoyin hadaka ke takawa wajen bunkasa tattalin arziki da ci gaban al’umma, da kuma karfafa jama’a a kasar.
Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana hakan yayin kaddamar da shirin horo na musamman ga shugabanni, kwamitocin gudanarwa, da manajoji na kungiyoyin hadaka a Najeriya, wanda aka shirya a Kaduna.
A cewar Kungiyar Hadaka ta Duniya (International Cooperative Alliance), sama da kashi 12% na al’ummar duniya suna cikin daya daga cikin kungiyoyin hadaka miliyan 3 a duniya.
Kungiyoyin hadaka suna nada muhimmiyar gudunmuwa wajen bunkasa tattalin arziki mai dorewa, inda suke samar da ayyukan yi da damammaki ga mutane miliyan 280, wanda ya kai kimanin kashi 10% na ma’aikatan duniya.
Kungiyoyin hadaka 300 mafi girma da kamfanonin taimakon juna suna samar da kudaden shiga har dala tiriliyan 2.4, kamar yadda rahoton World Cooperative Monitor na 2023 ya nuna.
A cewar Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, domin cika burin farfado da wannan bangare, Gwamnatin Tarayya ta kuduri aniyar samar da horo da damammakin ci gaban shugabanni da manajoji na kungiyoyin hadaka a jihohi 36 na Tarayya ciki har da Babban Birnin Tarayya (FCT).
Ya ce yayin da gwamnati ke aiwatar da Shirin Sabon Fata don bangaren kungiyoyin hadaka, tana daukar matakan gyara da farfado da tsarin domin mayar da martabar kungiyoyin hadaka a matsayin mai karfi wajen ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.
Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya kuma bayyana cewa gyaran zai mayar da hankali kan dubawa da gyaran dokar Nigeria Cooperative Act don daidaita ta da kyawawan dabi’un duniya da yanayin gida.
Samar da tsari mai kyau na lura da gudanarwar kungiyoyin hadaka don tabbatar da gaskiya da rikon amana.
Samar da tsare-tsaren sa ido don kawar da kungiyoyin hadaka na bogi da masu zamba.
Ya kuma yaba wa Shugaban Kwalejin Hadaka ta Tarayya Kaduna, Dakta Ibrahim Auwal, bisa kaddamar da wannan shirin horo na musamman da ya yi daidai da tsarin gyara da farfado da bangaren.
A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin, Dakta Ibrahim Auwal, ya ce horon zai baiwa mahalarta damar samun kwarewa da ilimin da ake bukata don ci gaban kungiyoyinsu da karfafa al’ummomin da suke wakilta.
Ya jaddada cewa kungiyoyin hadaka su ne ginshikan karfafa tattalin arziki da hade-haden zamantakewa, da ci gaba mai dorewa.
Cov: Adamu Yusuf
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
