Connect with us

Labarai

Gwamnati Ta Tabbatarda Kungiyoyin Hadaka A Matsayin Ginshikin Ci gaban Al’umma

Published

on

 

Gwamnatin Tarayya ta ce ta gano irin muhimmiyar gudunmuwar da kungiyoyin hadaka ke takawa wajen bunkasa tattalin arziki da ci gaban al’umma, da kuma karfafa jama’a a kasar.

 

Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya bayyana hakan yayin kaddamar da shirin horo na musamman ga shugabanni, kwamitocin gudanarwa, da manajoji na kungiyoyin hadaka a Najeriya, wanda aka shirya a Kaduna.

 

A cewar Kungiyar Hadaka ta Duniya (International Cooperative Alliance), sama da kashi 12% na al’ummar duniya suna cikin daya daga cikin kungiyoyin hadaka miliyan 3 a duniya.

 

Kungiyoyin hadaka suna nada muhimmiyar gudunmuwa wajen bunkasa tattalin arziki mai dorewa, inda suke samar da ayyukan yi da damammaki ga mutane miliyan 280, wanda ya kai kimanin kashi 10% na ma’aikatan duniya.

 

Kungiyoyin hadaka 300 mafi girma da kamfanonin taimakon juna suna samar da kudaden shiga har dala tiriliyan 2.4, kamar yadda rahoton World Cooperative Monitor na 2023 ya nuna.

 

A cewar Karamin Ministan Noma da Tsaron Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, domin cika burin farfado da wannan bangare, Gwamnatin Tarayya ta kuduri aniyar samar da horo da damammakin ci gaban shugabanni da manajoji na kungiyoyin hadaka a jihohi 36 na Tarayya ciki har da Babban Birnin Tarayya (FCT).

 

Ya ce yayin da gwamnati ke aiwatar da Shirin Sabon Fata don bangaren kungiyoyin hadaka, tana daukar matakan gyara da farfado da tsarin domin mayar da martabar kungiyoyin hadaka a matsayin mai karfi wajen ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a Najeriya.

 

Dakta Aliyu Sabi Abdullahi ya kuma bayyana cewa gyaran zai mayar da hankali kan dubawa da gyaran dokar Nigeria Cooperative Act don daidaita ta da kyawawan dabi’un duniya da yanayin gida.

 

Samar da tsari mai kyau na lura da gudanarwar kungiyoyin hadaka don tabbatar da gaskiya da rikon amana.

 

Samar da tsare-tsaren sa ido don kawar da kungiyoyin hadaka na bogi da masu zamba.

Ya kuma yaba wa Shugaban Kwalejin Hadaka ta Tarayya Kaduna, Dakta Ibrahim Auwal, bisa kaddamar da wannan shirin horo na musamman da ya yi daidai da tsarin gyara da farfado da bangaren.

 

A nasa jawabin, Shugaban Kwalejin, Dakta Ibrahim Auwal, ya ce horon zai baiwa mahalarta damar samun kwarewa da ilimin da ake bukata don ci gaban kungiyoyinsu da karfafa al’ummomin da suke wakilta.

 

Ya jaddada cewa kungiyoyin hadaka su ne ginshikan karfafa tattalin arziki da hade-haden zamantakewa, da ci gaba mai dorewa.

 

Cov: Adamu Yusuf

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara