Ilimi
Gwamnan Neja Ya Bada Umarnin Sake Bude Jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida, Lapai.
Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja ya bayar da umarnin bude jami’ar Ibrahim Badamasi Babangida Lapai domin fara gudanar da karatu na yau da kullun.
Umurnin sake bude jami’ar ya biyo bayan nazari sosai kan matakan tsaro da inganta ababen more rayuwa a jami’ar.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Neja Alhaji Abubakar Usman ya rabawa manema labarai ta hannun jami’in yada labaran sa Lawal Tanko a Minna.
Ya ce Gwamna Bago ya gamsu da ingantaccen gine-ginen tsaro da ci gaban ababen more rayuwa da aka yi don kare dalibai da ma’aikata da kuma al’ummar Jami’ar.
Sakataren Gwamnan Jihar Neja dai ya jaddada jajircewar Gwamnati wajen kare jin dadin dalibai da ma’aikata tare da tabbatar da ci gaban ilimi ba tare da katsewa ba.
Alhaji Abubakar Usman ya yaba da kokarin hadin gwiwa da jami’an tsaro da hukumomin jami’ar da shugabannin al’umma ke yi wajen magance kalubalen da ya kai ga rufe jami’ar.
A cewarsa, “Gwamna Bago, yayin da yake amincewa da sake bude taron, ya jaddada cewa, tsaro da jin dadin dalibai da ma’aikata su ne babban fifiko ga gwamnatinsa, ya kuma jaddada kudirinsa na inganta ilimi a matsayin ginshikin ci gaba, tare da tabbatar wa al’ummar Jami’ar goyon bayan gwamnati”.
Sanarwar ta yi kira ga daukacin dalibai da ma’aikatan da suka dawo da su bi ka’idojin tsaro da kuma bayar da cikakken hadin kai ga mahukuntan Jami’ar domin a sami zaman lafiya.
An rufe jami’ar na wani dan lokaci ne saboda matsalar tsaro da kuma asarar rayuka da aka yi a tsakanin al’ummar jami’ar, wanda a yanzu ake sa ran za a ci gaba da aiki a yau Litinin 4 ga watan Agusta ashirin da biyar.
ALIYU LAWAL
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
