Labarai
Gobara Ta Hallaka Mutane Arba’in Da Daya A Kuwait
Wata gobara da ta tashi a wani gidan ma’aikata da ke garin Mangaf na kasar Kuwait, ta hallaka mutane 41, kamar yadda mataimakin firai ministan kasar Sheikh Fahad Yusuf Saud Al-Sabah ya tabbatar.
Cikin wani jawabi da mataimakin firai ministan ya yi, ya ce gidan matattara ce ta mutane da ke kananan ayyuka a kasar, wanda mafi akasarin su bakaken fata ne.
Sheikh Al-Sabah ya alakanta tashin gobarar da tsantsar son zuciya da kuma rashin bin ka’ida da wasu dillalan da ke bada gidajen haya ke nunawa.
Bayanai sun ce wutar ta tashi da misalin karfe 6 na safiyar Laraba agogon kasar, kamar yadda Manjo Janar Eid Rasheed Hamad daya daga cikin mahukuntan kasar ya tabbatar.
Ya ce an yin nasarar ceto wasu da dama, yayin da wasu suka gamu da munanan raunuka, sai dai kuma abin tashin hankalin shi ne yadda wutar ta kona mutane 41 kurmus.
Manjo janar Rasheed ya ce kowanne lokaci hukuma na iya bakin kokarinta wajen ganin ta rage cinkoso a irin wadannan gidaje, amma masu bada haya sai su yi amfani da barauniyar hanya wajen tara mutane kawai don neman kudi.
Har yanzu dai babu cikakken bayani kan musabbabin tashin gobarar sai dai jami’ai na ci gaba da bincike.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
