Connect with us

Labarai

Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.

Published

on

Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello ta sanar da cewa za ta gudanar da bikin tunawa da Sir Ahmadu Bello na shekara karo na 11 a ranar Litinin, 24 ga Fabrairu, 2025, a Bauchi, Jihar Bauchi.

Taron, wanda aka shirya tare da hadin gwiwar Gwamnatin Jihar Bauchi, zai girmama marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sakkwato kuma Firaministan tsohuwar Yankin Arewa.

A bana, taken laccar shi ne “Arzikin Halitta: Juya Albarkatun Yankin Arewa Zuwa Ci Gaban Tattalin Arziki Mai Dorewa.”

Tattaunawar za ta mayar da hankali ne kan yadda za a yi amfani da albarkatun noma da ma’adanai da ruwa don bunkasa ci gaban tattalin arzikin yankin.

Duba da kalubalen tattalin arzikin da Najeriya ke fuskanta, musamman yankin Arewa, laccar za ta bayyana rawar da gwamnati da ɓangarori masu zaman kansu da kungiyoyin al’umma za su taka wajen inganta sarrafa albarkatu da bunkasa darajar kayayyaki da samar da ayyukan yi.

Babbar lacca za a gabatar da ita ne daga bakin Dr. Mansur Mukhtar (Sarkin Bai Kano), tsohon Mataimakin Shugaban Bankin Musulunci kuma Shugaban Bankin Masana’antu na Najeriya.

Ana sa ran Sanata George Akume, Sakataren Gwamnatin Tarayya, zai kasance Babban Bako na Musamman a wurin taron.

Haka nan, ana sa ran halartar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, wanda shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa, kuma zai jagoranci taron.

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, zai kasance Babban Mai Masaukin baki. Haka kuma, ana sa ran halartar gwamnonin jihohi da ministoci da ‘yan majalisa da sarakuna da sauran manyan baki daga sassa daban-daban.

A cewar Darakta-Janar na Gidauniyar, Injiniya Dr Abubakar Gambo Umar, albarkatun yankin Arewa na da babban damar sauya tattalin arzikin yankin.

“Sai dai dole mu dauki matakan da za su tabbatar da sarrafa albarkatunmu cikin adalci da dorewa, domin amfanin kowa da kowa,” in ji shi.

A yayin taron, gidauniyar za ta bayar da tallafin karatu ga dalibai marasa galihu daga Jihar Bauchi da ke karatu a manyan makarantu domin tallafa musu.

Bugu da kari, za a karrama wasu fitattun mutane da lambar yabo saboda gudunmawar da suka bayar ga cigaban al’umma.

Har ila yau, za a gudanar da shirin ba da agajin lafiya domin samar da hidimar kiwon lafiya ga al’ummar yankin.

Gidauniyar Tunawa da Sir Ahmadu Bello an kafa ta ne domin ci gaba da girmama gadon shugabanci da ilimi da ci gaban tattalin arziki da marigayi Sardaunan Sakkwato ya assasa.

Bikin tunawa na kowace shekara, wanda ke gudana a jihohi 19 na Arewa, na zama wata kafa ta tattaunawa kan ci gaban yankin da shugabanci.

Gidauniyar ta nemi afuwar duk wani rashin jin dadi da sauya ranar taron ka iya haifarwa, tare da gode wa duk masu mara mata baya.

Rel: Khadija Kubau

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara