Connect with us

Kasuwanci

Gazawar Shugaba Bola Tinibu Ne Ya Sa Sanata Marafa Ficewa Daga APC

Published

on

Shugaban kungiyar goyon bayan Sanata Marafa, Alhaji Surajo Garba Maikatako, ya ce ficewar Sanata Kabir Garba Marafa daga jam’iyyar APC ya kara karfafa masa siyasa tare da jaddada goyon bayansa ga magoya bayansa.

 

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun sa da kan sa, Alhaji Maikatako ya bayyana cewa Sanata Marafa ya yanke shawarar ficewa daga jam’iyyar APC ba wani yunkuri ne na kashin kai ba, sai dai an dauki matakin ne na gama-gari bayan tattaunawa da magoya bayan sa.

 

Ya ce tun bayan wannan sanarwar kungiyar ta fara samun sakonni da ziyarce-ziyarcen hadin kai daga fadin jihar Zamfara da Arewa maso Yamma da kuma wajenta, inda da yawa ke bayyana shirin tafiya da sabuwar alkiblar siyasa.

 

A cewarsa, wannan ci gaban alheri ne kuma ya zama wani sauyi a tafiyarsu ta siyasa.

 

Alhaji Surajo Garba Maikatako ya bayyana Sanata Marafa a matsayin daya daga cikin shugabanni masu kishin kasa kuma masu hangen nesa wadanda siyasarsu ta ginu akan adalci, rikon amana da yiwa al’umma hidima.

 

Alhaji Maikatako ya ci gaba da cewa, sabanin ikirari da shugabannin jam’iyyar APC na Zamfara ke yi, Sanata Marafa yana samun goyon bayan talakawa, inda ya ce har yanzu jam’iyyar ba ta lamunta da ficewar sa.

 

Ya yi zargin cewa jam’iyyar APC a Zamfara ta rasa nasaba da siyasa, inda ya nanata cewa, wadanda ake yi wa lakabi da wadanda za su maye gurbin Sanata Marafa ba su da ra’ayin jama’a kuma ba za su iya gabatar da zaben jam’iyyar nan gaba ba.

 

Shugaban kungiyar ya kuma alakanta ficewar Sanata Marafa da gazawar shugaban kasa Bola Tinubu wajen cika alkawuran yakin neman zabe, musamman kan rashin tsaro a jihar Zamfara, duk kuwa da rawar da Sanatan ke takawa a matsayin kodinetan yakin neman zaben jihar a zaben 2023.

 

Ya kuma jaddada cewa kungiyar tasu a yanzu tana shirye-shiryen wani abin da ya bayyana a matsayin yakin neman zaben shugaban kasa mai cike da tarihi, inda ya bukaci magoya bayansa da ‘yan Najeriya masu kishin kasa da su hada kai wajen kwato mulkin dimokaradiyya da dawo da martabar mulki.

REL/AMINU DALHATU.

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara