Connect with us

Labarai

Cibiyar Ilimin ’Ya’ya Mata Ta Buƙaci Ci Gaba da Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata

Published

on

Cibiyar Ilimin ’Ya’ya Mata ta yi kira ga iyaye, shugabannin gargajiya da na addini da su ci gaba da bayar da goyon baya wajen inganta ilimin ’yan mata masu tasowa.

Mai Kula da Ayyukan Cibiyar, Malama Alawiya Abdullahi, ta yi wannan kiran ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki na kwana guda, da aka gudanar a dakin taro na cibiyar da ke Sabon Gari GRA a Zariya.

Malama Alawiya Abdullahi ta bayyana cewa shirin ya mayar da hankali ne kan bai wa ’yan mata masu shekaru daga goma sha ɗaya zuwa goma sha shida ilimin karatu da lissafi, musamman waɗanda ba sa zuwa makaranta ko kuma suka daina zuwa.

Ta ƙara da cewa taron shi ne karo na huɗu da cibiyar ta shirya domin tantance ci gaban aikin, tattauna ƙalubale da kuma ƙarfafa mallakar shirin daga al’umma.

Saboda haka, mai kula da aikin ta yi kira ga sarakunan gargajiya da limamai da su ƙara wayar da kan al’umma, tare da ƙarfafa iyaye su bai wa ’ya’yansu mata damar samun ingantaccen ilimi.

Wasu daga cikin masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yaba da shirin, suna bayyana yadda ya samar da alfanu mai yawa ga al’ummominsu, musamman wajen faɗaɗa damar ilimi ga ’ya’yansu mata.

Maharta taron sun yanke shawarar yin aiki tare domin bunƙasa ilimin ’yan mata da kuma tabbatar da ɗorewar shirin a cikin al’ummominsu.

A yayin taron, mahalarta sun bayar da shawarwari tare da shiga tattaunawar rukuni-rukuni da jami’an shirin suka jagoranta.

Taron ya samu halartar mahalarta daga ƙananan hukumomin Giwa, Makarfi, Sabon Gari da Zariya.

Ibrahim Suleiman/Zaria

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara