Labarai
APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara ta yi kakkausar suka ga gwamna Dauda Lawal kan kalaman da ta bayyana a matsayin bata gari dangane da kokarin gwamnatinsa na magance ‘yan fashi da makami da kuma bayar da tallafi ga wadanda ‘yan fashin suka kashe.
Hakan ya biyo bayan wani faifan bidiyo ne da aka ga gwamnan yana magana da manema labarai kan yadda gwamnatinsa ke tafiyar da harkokin tsaro da kuma jin dadin wadanda matsalar tsaro ta shafa.
A wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar APC, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya bayyana kalaman gwamnan a matsayin rashin gaskiya da yaudara.
Malam Idris Yusuf Gusau ya yi zargin cewa, gwamnatin ta gaza cika wasu muhimman alkawuran yakin neman zabe, musamman alkawarin kawo karshen ‘yan fashi da makami a cikin watanni biyun farko da fara aiki.
Sanarwar ta kara da cewa “Gwamna Lawal da alama yana shirin cika shekara biyu a kan karagar mulki ba tare da samun wani ci gaba mai ma’ana ba kan babban alkawarin da ya yi a yakin neman zabe, maimakon a samu ci gaba, matsalar tsaro ta ta’azzara a Zamfara.”
A cewar Yusuf Idris, kalaman gwamna Lawal na baya-bayan nan a babban asibitin Gusau sun nuna rashin tausayi da jin kai.
“Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnan da yin watsi da wadanda harin ya rutsa da su. “Maimakon ya ziyarci al’ummomin da ‘yan bindiga suka lalata ko aika sahihan tawaga don jajantawa da bayar da goyon baya, Gwamna Lawal ya zabi tafiya daga wata jiha ko kasa zuwa wata, yana jin dadin abokansa da ‘yan uwa yayin da mutanensa ke shan wahala.”
Ya yi nuni da cewa, babban abin da ya jawo cece-kuce shi ne ikirarin da gwamnan ya yi na cewa wadanda suka samu raunukan harbin bindiga suna karbar magani kyauta a asibitin kwararru na Yariman Bakura da cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Gusau.
“Wannan karya ce kawai,” in ji Idris. “A makonnin da suka gabata ni da kaina na ga wadanda lamarin ya rutsa da su an mayar da su asibitin Yariman Bakura saboda rashin kudi, abin takaici wasun su sun mutu sakamakon haka, ba tare da taimakon gwamnati ba.”
Jam’iyyar APC ta yi kira ga gwamnan da ya fito fili ya bayyana sunaye, al’ummomi, da bayanan kula da wadanda suka ci gajiyar da aka ce sun samu kulawa kyauta, ciki har da kudaden da aka kashe da kuma kudaden da suka dace ko kuma bayanan biyan su.
Kakakin jam’iyyar APC ya kuma bukaci Gwamnan da mahukuntan asibitocin biyu da su buga cikakkun bayanai na jinya kyauta da aka yi a karkashin gwamnatinsa.”
Jam’iyyar ta kuma bukaci ‘yan jaridan da suka gudanar da hirar da su tabbatar da ikirarin gwamnan tare da zurfafa bincike kan al’amuran da abin ya shafa a lunguna da sako na jihar, kamar karamar hukumar Tsafe, wadanda ba za su iya samun kayan aiki a Gusau ba.
REL/AMINU DALHATU.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
