Labarai
Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka
Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran mai suna IRIS Dena da safiyar yau Laraba.
Mai magana da yawun rundunar, Budhika Sampath, ya ce ko da yake lamarin ya faru ne a wajen iyakar ruwan ƙasarsu, amma yana cikin yankin da suke da alhakin aikin ceto, don haka wajibi ne su amsa kiran bisa ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.
Ya ce sun tarar da wasu mutane na shawagi a kan ruwa, inda suka ceto su, sannan daga bisani bincike ya nuna cewa mutanen na cikin jirgin ruwan Iran din ne.
A cewarsa, takardun jirgin sun nuna cewa kimanin mutum 180 ne ke cikinsa, sai dai har yanzu ba a tabbatar da ainihin adadin waɗanda suka ɓace ba.
Tun da fari, sakataren ma’aikatar tsaron ƙasar, Air Vice Marshal Sampath Thuiyakontha, ya shaida wa BBC cewa ana kyautata zaton kusan mutum 140 sun ɓace.
Mai magana da yawun rundunar ya ƙara da cewa a lokacin da suka isa wurin domin aikin ceto, ba su hangi jirgin ba, amma sun ga tabon mai a saman ruwa da kuma kwale-kwalen ceton rai na shawagi.
Ya zuwa yanzu, rundunar sojin ƙasar ba ta iya tabbatar da abin da ya haddasa nutsewar jirgin ba.
BBC
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
