Connect with us

Kasuwanci

An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.

Published

on

Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kama wasu mutane shida da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da ke gudanar da ayyukansu a karamar hukumar Toro ta jihar tare da ceto wasu mutane uku da aka sace ba tare da komi ba.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), CSP Mohammed Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Bauchi.

 

A cewar sanarwar, rundunar ‘yan sandan ta samu kiran gaggawa daga wani dan banga da ke kauyen Euga da misalin karfe 12:01 na safiyar ranar 29 ga watan Satumba, 2025, inda ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun yi awon gaba da wasu mutane uku wato Idi Umar, Idi Lawan, da Musa Lawal.

 

Wakil ya ce “A martanin da aka mayar, an kaddamar da wani aiki na hadin gwiwa wanda ya hada da rundunar ‘yan sanda ta Toro, Toro Division, Nabordo Division, da kuma jami’an tsaro na cikin gida.”

 

Ya kara da cewa rundunar hadin guiwa ta bin diddigin wadanda ake zargin har zuwa wajen kauyen, inda suka gudanar da wani samame na dabara wanda ya kai ga ceto wadanda lamarin ya rutsa da su tare da kama wasu mutane shida da ake zargi.

 

Wadanda aka kama sun hada da Abubakar Usman, Adamu Alo, Abubakar Aliyu, Umar Habu, Abubakar Mamman Abubakar, da Shehu Sambo.

 

Karshen/Alhassan.

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara