Labarai
An Bukaci Musulmi Su Yi Amfani da Darussan Ramadan — Janar Abdulsalami
Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar (mai ritaya), ya buƙaci al’ummar Musulmi da su aiwatar da darussan da suka koya a watan Ramadan domin inganta rayuwarsu.
Janar Abdulsalami ya yi wannan kira ne bayan gudanar da sallar Idi raka’o’i biyu ta Eid-el-Fitr a filin sallar Idi na Minna, Jihar Neja.
Ya kuma ƙara da cewa ya kamata Musulmi su ci gaba da taimakon juna tare da nuna ƙauna da jin ƙai ga marasa galihu, bisa koyarwar addinin Musulunci.
A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da gargaɗin matasa a jihar da su kasance masu natsuwa, su guji duk wani abu da zai iya tayar da tarzoma yayin bikin Sallah.
Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba, wanda ya wakilce shi, ya ce gwamnan yana cikin gari, kuma daga bisani zai je fadar Sarkin Minna, Dakta Umar Faruk Bahago, domin halartar bikin durbar.
Shi ma tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dakta Mu’azu Babangida Aliyu, ya tunatar da Musulmi cewa daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar, azumi ne kaɗai Allah Ya ce nasa ne kai tsaye, kuma Shi ne zai ba da lada ga duk wanda ya yi shi yadda ya kamata.
Sai dai ya buƙaci Musulmi da su bayar da Zakatul Fitr ga masu buƙata domin su samu abin da za su ciyar da iyalansu a ranar Sallah.
Aliyu Lawal/ Minna
-
Labarai3 days agoAdalci a Kauru LGA Yayin da Tsarin Raba Mukamai ke Kara Karɓuwa Domin Wakilci Nagari
-
Labarai5 days agoHukumar Alhazan Jihar Jigawa ta Kaddamar da Kwamitin Amirul Hajjin Bana
-
Labarai2 days agoRadio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya
-
Labarai7 days agoTrump Ya Aike da Daftarin Shirin Zaman Lafiya ga Iran
-
Labarai2 days agoMasarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin
-
Labarai2 days agoHukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana
-
Labarai5 days agoHajjin2026: Jigawa ta Kara Kaimi Wajen Horar Da Maniyyata
-
Labarai2 days agoƊaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano
