Connect with us

Labarai

An Bukaci Musulmi Su Yi Amfani da Darussan Ramadan — Janar Abdulsalami

Published

on

Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar (mai ritaya), ya buƙaci al’ummar Musulmi da su aiwatar da darussan da suka koya a watan Ramadan domin inganta rayuwarsu.

Janar Abdulsalami ya yi wannan kira ne bayan gudanar da sallar Idi raka’o’i biyu ta Eid-el-Fitr a filin sallar Idi na Minna, Jihar Neja.

Ya kuma ƙara da cewa ya kamata Musulmi su ci gaba da taimakon juna tare da nuna ƙauna da jin ƙai ga marasa galihu, bisa koyarwar addinin Musulunci.

A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya taya Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da gargaɗin matasa a jihar da su kasance masu natsuwa, su guji duk wani abu da zai iya tayar da tarzoma yayin bikin Sallah.

Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba, wanda ya wakilce shi, ya ce gwamnan yana cikin gari, kuma daga bisani zai je fadar Sarkin Minna, Dakta Umar Faruk Bahago, domin halartar bikin durbar.

Shi ma tsohon Gwamnan Jihar Neja, Dakta Mu’azu Babangida Aliyu, ya tunatar da Musulmi cewa daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar, azumi ne kaɗai Allah Ya ce nasa ne kai tsaye, kuma Shi ne zai ba da lada ga duk wanda ya yi shi yadda ya kamata.

Sai dai ya buƙaci Musulmi da su bayar da Zakatul Fitr ga masu buƙata domin su samu abin da za su ciyar da iyalansu a ranar Sallah.

Aliyu Lawal/ Minna

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara