Connect with us

Labarai

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Published

on

Daga Khadijah Aliyu

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da suka maƙale a ƙasashen waje, waɗanda aka dawo da su daga Niamey, Jamhuriyar Nijar, a matsayin wani ɓangare na shirin dawo da ’yan ƙasa na son rai da Gwamnatin Tarayya ke gudanarwa.

An kawo waɗanda aka dawo da su cikin motoci kirar bas guda 12, inda suka isa Filin Jirgin Sama na Malam Aminu Kano da misalin ƙarfe 5 da minti 10 na yamma, inda jami’ai suka tarbe su tare da yi musu rijista da tantancewa.

Da yake magana da manema labarai a filin jirgin saman, Shugaban Ayyuka na NEMA a ofishin Kano, Dakta Nura Abdullahi, ya ce an dawo da mutanen ne bisa son ransu, ba tare da an tilasta su ba.

Abdullahi ya bayyana cewa waɗanda aka dawo da su sun haɗa da  maza 267, da mata 101, sai yara maza 82, da yara mata 72, daga jihohi daban-daban ciki har da Kano, Jigawa, Filato da Bauchi.

Ya ƙara da cewa NEMA tare da haɗin gwiwar sauran masu ruwa da tsaki sun tanadi dukkan matakan da suka dace domin kula da waɗanda aka dawo da su bayan isowarsu.

A cewarsa, da dama daga cikin waɗanda aka dawo da su sun yi hijira ne ba bisa ƙa’ida ba, domin neman ingantacciyar rayuwa, inda suka nufi ƙasashe kamar Libya da Aljeriya, amma suka bukaci dawowa  gida bayan fuskantar ƙalubale a hanya.

Abdullahi ya kuma ce an tanadi wuraren zama na wucin gadi, tare da raba muhimman kayan agaji kamar abinci, bargo, gidan sauro, da kayan tsafta  na mata (dignity kits) ga waɗanda aka dawo da su.

Shi a nasa jawabin, wakilin Ma’aikatar Harkokin Waje ta Tarayya, Malam Magaji Umar, ya yaba wa Gwamnatin Tarayya kan sauƙaƙa dawowar ’yan ƙasar cikin aminci.

Ya ce wannan shiri ya yi daidai da manufofin ƙasa kan harkokin hijira, da kuma ƙudirin gwamnati na kare ’yan Najeriya a ƙasashen waje.

Umar ya ƙara da cewa wannan aiki ya samu nasara ne sakamakon haɗin gwiwar manyan hukumomi da suka haɗa da Ma’aikatar Harkokin Waje, ofisoshin jakadancin Najeriya, da Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Duniya (IOM).

Hukumar ta NEMA  ce ta tarbi waɗanda aka dawo da su  tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi da suka haɗa da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA), Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira (NCFRMI), Kungiyar Red Cross ta Najeriya, da Hukumar Shige da Fice ta Najeriya.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara