Labarai
Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da masu karɓar fansho a faɗin jihar, gabanin bikin Sallar Eid-el-Fitr.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu, Mahmud Muhammad Dantawasa ya fitar, ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin saukaka wa ma’aikata da wadanda suka yi ritaya, tare da ba su damar yin shirye-shiryen Sallah yadda ya kamata.
Dantawasa ya bayyana cewa, bisa ga bayanin da aka samu daga Ofishin Akanta Janar na Jihar, an kammala dukkan shirye-shirye da suka dace domin tabbatar da an biya albashi da fansho cikin gaggawa ga dukkan waɗanda suka cancanta a faɗin jihar.
Ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na ci gaba da kula da jin daɗin ma’aikatan gwamnati da ‘yan fansho, tare da yaba musu bisa sadaukarwa da gudummawar da suke bayarwa wajen ci gaban Jihar Zamfara.
Mahmud Dantawasa ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ba da fifiko ga manufofin da za su inganta rayuwar ma’aikata da wadanda suka yi ritaya.
Haka kuma ya buƙaci ma’aikatan gwamnati da ‘yan fansho da su ci gaba da mara wa manufofin gwamnati baya, tare da yin addu’ar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Zamfara.
Gwamnatin Jihar Zamfara ta kuma yi wa dukkan ma’aikatan gwamnati, da wadanda suka yi ritaya, da kuma al’ummar jihar fatan yin Sallar Eid-el-Fitr cikin kwanciyar hankali da farin ciki.
-
Labarai6 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai6 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
-
Labarai6 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai4 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai4 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai4 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai4 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai1 day agoJIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah
