Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Published

on

Daga Aminu Dalhatu

Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da masu karɓar fansho a faɗin jihar, gabanin bikin Sallar Eid-el-Fitr.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Al’adu, Mahmud Muhammad Dantawasa ya fitar, ya ce an ɗauki wannan mataki ne domin saukaka wa ma’aikata da wadanda suka yi ritaya, tare da ba su damar yin shirye-shiryen Sallah yadda ya kamata.

Dantawasa ya bayyana cewa, bisa ga bayanin da aka samu daga Ofishin Akanta Janar na Jihar, an kammala dukkan shirye-shirye da suka dace domin tabbatar da an biya albashi da fansho cikin gaggawa ga dukkan waɗanda suka cancanta a faɗin jihar.

Ya kuma jaddada ƙudirin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na ci gaba da kula da jin daɗin ma’aikatan gwamnati da ‘yan fansho, tare da yaba musu bisa sadaukarwa da gudummawar da suke bayarwa wajen ci gaban Jihar Zamfara.

Mahmud Dantawasa ya tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da ba da fifiko ga manufofin da za su inganta rayuwar ma’aikata da wadanda suka yi ritaya.

Haka kuma ya buƙaci ma’aikatan gwamnati da ‘yan fansho da su ci gaba da mara wa manufofin gwamnati baya, tare da yin addu’ar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa a Jihar Zamfara.

Gwamnatin Jihar Zamfara ta kuma yi wa dukkan ma’aikatan gwamnati, da wadanda suka yi ritaya, da kuma al’ummar jihar fatan yin Sallar Eid-el-Fitr cikin kwanciyar hankali da farin ciki.

Labarai

Labarai14 hours ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai18 hours ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai22 hours ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai23 hours ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai1 day ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai1 day ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai1 day ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai1 day ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai4 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai4 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara