Connect with us

Labarai

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa kokarinsu na hadin gwiwa wajen samun nasarar rabon kayan abinci na watan Ramadan a kananan hukumomi 14 na jihar, domin tallafa wa marasa galihu da marayu.

Ta yi wannan yabon ne a lokacin rabon kayan a karamar hukumar Gusau, inda ta bayyana cewa an tsara shirin ne domin rage radadin rayuwa ga iyalai a wannan wata mai alfarma na Ramadan.

A cewarta,  rabon ya shafi dukkan kananan hukumomin jihar, inda aka fara daga Shinkafi da Zurmi, sannan Birnin Magaji da Kaura Namoda, daga nan sai Gummi da Bukkuyum, Anka da Talata Mafara, Maradun da Bakura, Maru da Bungudu, sannan aka kammala a Tsafe da Gusau.

Hajiya Huriyya ta bayyana cewa an samu nasarar raba kunshin kayan abinci guda 50,000 a fadin jihar. Ta ce kowane kashi ya kunshi buhun shinkafa mai nauyin kilo 20, wake, masara da gero, da kilo 5 na sukari, taliya, man girki, gishiri, da kuma sutura ga mata.

Uwargidan gwamnan ta kuma bayyana cewa an kafa kwamitoci a matakin gunduma domin yin aiki tare da shugabannin kananan hukumomi, don tabbatar da adalci, gaskiya da rikon amana wajen rabon kayan.

Mun umurci kwamitocin da su gudanar da aikinsu da gaskiya, rikon amana da tsoron Allah, domin sauje amanar da aka dora musu ce,” in ji ta.

Ta kuma gode wa mambobin tawagarta da suka hada da direbobi, jami’an tsaro, daraktocin Zakka da ma’aikatansu, ‘yan jarida, masu aikin sa kai da duk wadanda suka bada gudunmawa wajen samun nasarar shirin.

Kun nuna jajircewa da sadaukarwa. Allah ne kadai zai saka wa kowa.” in ji ta.

Hajiya Huriyya ta kuma yaba wa Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa goyon bayansa da jajircewarsa wajen inganta jin dadin al’ummar jihar, tare da sauran masu taimako da suka taka muhimmiyar rawa wajen nasarar shirin.

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara