Labarai
Bankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta bada tabbacin baiwa bankin raya kasashen Afrika cikakken goyan bayan ta domin cika sharudda da ka’idojin da ake bukata domin amfanin al’ummar jihar.
Mataimakin Gwamnan jihar Injiniya Aminu Usman Gumel ya bada wannan tabbacin a lokacin da tawagar bankin ta ziyarci ofishin sa dake Dutse.

Yace Gwamnatin jihar ta himmatu wajen cika ka’idojin saboda muhimmancin su ga al’umma, musamman yadda jihar ta bi sahun wasu jihohi biyar da suke cikin shirin.
Tun farko a nasa jawabin, jagoran tawagar Bankin,ta bakin Babangida Shehu yace sun ziyarci ofishin mataimakin Gwamnan ne domin tattauna batutuwan da suka shafi cika sharuddan bankin, domin jihar ta samu nasarar amfana da tsare tsaren bankin a bangarorin bunkasa aikin gona da gina kamfanoni domin bunkasa tattalin arziki.
Ya kara da cewar tawagar bankin ta gamsu da tsare tsaren jihar Jigawa wajen cika ka’idojin a tsakanin sauran takwarorin ta jihohi biyar da suke cikin shirin.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoHukumar Alhazai ta Jigawa ta Jinjinawa Hukumomin Tsaro Bisa Goyon Bayan da Suke Ba Ta
