Connect with us

Labarai

Gwamna Kefas Na Taraba Ya Karbi Katin Jam’iyyar APC

Published

on

Daga Jamila Abba 

Gwamnan Jihar Taraba, Dakta Agbu Kefas, ya karɓi katin shaidar zama dan jam’iyyar APC a hukumance, wanda hakan ya tabbatar da cikakken rajistarsa cikin jam’iyyar.

An mika katin membobinsa na APC ga Gwamnan ne ta hannun Shugaban APC a gundumar Asibiti (Hospital Ward) da ke Karamar Hukumar Wukari, Honarabul Umaru Tanko ne ya mika katin zama mamban na APC ga Gwamna Kefas a gidan TY Danjuma da ke Jalingo.

Da yake jawabi a ofishinsa bayan karɓar katin, Gwamna Kefas ya bayyana cewa rajistarsa ta tabbatar da matsayinsa a hukumance a matsayin cikakken mamba na APC, wanda hakan zai ba shi damar shiga dukkan harkokin jam’iyyar.

Ya ƙara da cewa nan ba da jimawa ba za a yi bikin sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar ta APC.

A yayin mika katin, Honarabul Umaru Tanko ya bayyana Gwamnan a matsayin cikakken mamba na APC tare da nuna farin cikin jam’iyyar na maraba da shi a hukumance.

Haka kuma, Kwamishinar yada Labarai da Wayar da Kai ta Jihar, Barista Zainab Usman Jalingo, ta tabbatar da cewa yanzu Gwamna Kefas cikakken mamba ne na APC a Jihar Taraba.

 

 

 

Labarai

Labarai1 day ago

Gidauniyar NASARA Ta Raba Kayayyakin Ramadan da na Sallah ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Marayu da zawarawa sama da dubu ɗaya ne suka amfana da tallafin kayayyakin Ramadana da na Sallah...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Rantsar da Taiwo Oyedele Ministan Kudi

Daga Bello Wakili  Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Taiwo Oyedele a matsayin  Minista a Ma’aikatar. An gudanar...

Labarai2 days ago

Yi Wa Shuwagabanni Biyayya Ne Zai Kai mu Ga Ci Gaba – Garkuwan Kudun Zazzau

Dokta Muhammad Sani Uwaisu FCNA, Garkuwan Kudun Zazzau, ya yi kira ga daukacin al’ummar Musulmin Duniya baki daya da su...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Zamfara Ta Amince da Biyan Albashin Watan Maris Gabanin Bukukuwan Karamar Sallah

Daga Aminu Dalhatu Gwamnatin Jihar Zamfara ta amince da biyan albashin watan Maris da wuri ga dukkan ma’aikatan gwamnati da...

Labarai2 days ago

Mambobin APC Sun Kai 158,697 a Zamfara Bayan Sauya Shekar Gwamna Lawal

Adadin mambobin jam’iyyar APC a jihar Zamfara ya karu zuwa 158,697, kwanaki uku kacal bayan sake bude tsarin rajistar mambobi...

Labarai2 days ago

Kwara NUJ Iftar: An Bukaci ‘Yan Jarida Su Rika Tsayawa Kan Gaskiya

An bukaci ‘yan jarida su tabbatar rahotanninsu sun dogara da gaskiya tare da guje wa son zuciya domin kare mutuncinsu...

Labarai2 days ago

‘Yan Sanda Sun Bankado Maboyar Masu Garkuwa

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce ta samu wani gagarumin nasara a kokarinta na yaki da masu garkuwa da...

Labarai2 days ago

JIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah

Shugaban Majalisar Malamai ta ƙasa na ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bidi’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS), Ash Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya...

Labarai5 days ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai5 days ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Mafi Shahara