Labarai
Gwamna Kefas Na Taraba Ya Karbi Katin Jam’iyyar APC
Daga Jamila Abba
Gwamnan Jihar Taraba, Dakta Agbu Kefas, ya karɓi katin shaidar zama dan jam’iyyar APC a hukumance, wanda hakan ya tabbatar da cikakken rajistarsa cikin jam’iyyar.
An mika katin membobinsa na APC ga Gwamnan ne ta hannun Shugaban APC a gundumar Asibiti (Hospital Ward) da ke Karamar Hukumar Wukari, Honarabul Umaru Tanko ne ya mika katin zama mamban na APC ga Gwamna Kefas a gidan TY Danjuma da ke Jalingo.
Da yake jawabi a ofishinsa bayan karɓar katin, Gwamna Kefas ya bayyana cewa rajistarsa ta tabbatar da matsayinsa a hukumance a matsayin cikakken mamba na APC, wanda hakan zai ba shi damar shiga dukkan harkokin jam’iyyar.
Ya ƙara da cewa nan ba da jimawa ba za a yi bikin sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar ta APC.
A yayin mika katin, Honarabul Umaru Tanko ya bayyana Gwamnan a matsayin cikakken mamba na APC tare da nuna farin cikin jam’iyyar na maraba da shi a hukumance.
Haka kuma, Kwamishinar yada Labarai da Wayar da Kai ta Jihar, Barista Zainab Usman Jalingo, ta tabbatar da cewa yanzu Gwamna Kefas cikakken mamba ne na APC a Jihar Taraba.
-
Labarai6 days agoAn Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau
-
Labarai6 days agoTinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa
-
Labarai6 days agoKwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara
-
Labarai5 days agoKwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara
-
Labarai5 days agoJami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi
-
Labarai5 days agoAn Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya
-
Labarai5 days agoMatashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba
-
Labarai2 days agoJIBWIS Ta Bukaci Gwamna Bago Ya Gaggauta Sanya Hannu Kan Dokar Hisbah
