Kasuwanci
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gina Gadar Sama Da Ta Kasa A Mararraba
Gwamnatin Jihar Nasarawa ta ce ta samu amincewar gwamnatin tarayya domin gina sabbin gada biyu na sama da kuma ta karkashin kasa (under-pass) a yankin Mararaba da ke Karamar Hukumar Karu.
Babban Mataimaki na Musamman ga Gwamna Abdullahi Sule kan Harkokin Jama’a, Mr. Peter Ahemba, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.
A cewar Ahemba, gwamnati za ta fara aikin kafin gwamnatin yanzu ta kai ga karewar wa’adinta a shekara ta 2027. Ya ce tun da dadewa Gwamna Abdullahi Sule ya ware kudaden aikin, kafin ma a kammala tsarinsa.
Ya bayyana cewa, tun daga shekarar 2019, gwamnatin jihar ta kan ** tabbatar da ajiyar kuɗi kafin fara kowanne babban aiki**, saboda dorewa da tabbatar da kammalawa akan lokaci.
Ahemba ya ce gina wadannan flyovers da under-pass ya zama dole sakamakon cunkoson ababen hawa da ke addabar yankin Karu–Mararaba, musamman ga mazauna da direbobi da matafiya.
“Wannan aiki zai magance matsalar cunkoso, ya inganta tafiyar ababen hawa, tare da ƙara ingancin hanyoyi,” in ji shi.
Ya kara da cewa gwamna ya bai wa Hukumar Nasarawa State Urban Development Agency (NUDA) umarnin gudanar da bincike da tantance wuraren da suka fi dacewa domin gina wadannan ayyukan.
Mr. Ahemba ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta kuduri aniyar fara aikin, ta kuma kammala shi kafin karewar wa’adinta a 2027.
Aliyu Muraki, Lafia.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
