Kasuwanci
Majalisar Tattalin Arziki Ta Amince da Shirin Gyara Cibiyoyin Horar da Jami’an Tsaro
Majalisar Tattalin Arzikin Ƙasa (NEC) ta amince da shirin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu na sake fasalin da kuma zamanantar da cibiyoyin horar da jami’an tsaro a faɗin ƙasar. Wannan mataki ya biyo bayan taron majalisar na 152 da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, inda Ministan Tsare-tsaren Kasafi da Tattalin Arziki, Sanata Abubakar Atiku Bagudu, ya gabatar da jawabi kan dabarun cimma burin Shugaban Ƙasa na samar da tattalin arzikin da ya kai darajar dala tiriliyan guda.
An kafa kwamitin da Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ke jagoranta don tsara cikakken tsari na gyaran da sabunta cibiyoyin horar da jami’an ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro cikin wata guda. Mambobin kwamitin sun haɗa da gwamnonin jihohin Kaduna, Ogun, Taraba, Akwa Ibom, Zamfara, da Nasarawa, yayin da tsohon Sufeton ƴan sanda na ƙasa, Baba Usman, zai zama sakataren kwamitin.
Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin inganta yanayin cibiyoyin horar da jami’an tsaro domin ƙara ƙarfin horo da ƙwarewa tare da tabbatar da ƙwararru da ƙwarin gwiwar ma’aikatan tsaro.
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, wanda ya jagoranci taron, ya shawarci gwamnatocin jihohi su mai da hankali wajen inganta rayuwar jama’a ta hanyar gwamnati mai ma’ana da shiri na gaba. Haka kuma, majalisar ta duba bayanin da Ofishin Mai Ba da Shawara Kan Tsaron Ƙasa (ONSA) ya gabatar kan tsarin tunkarar matsalar ambaliyar ruwa, wanda ke da nufin ƙarfafa tsarin gargadin gaggawa da shirin kare jama’a daga ambaliyar ruwa a ƙasar baki ɗaya.
Dangane da burin tattalin arzikin gwamnati, Sanata Bagudu ya gabatar da taswirar cimma tattalin arzikin dala tiriliyan guda nan da shekarar 2033, wanda ke ta’allaka da daidaiton tattalin arziki, samar da ayyukan yi, wadatar abinci da inganta gasa tsakanin jihohi.
NEC ta kuma yaba da tsarin cimma Muradin aikin gona na jihar Katsina tare da shawartar sauran jihohi su rungumi irin wannan tsarin na fasaha domin ƙara yawan amfanin gona da haɗa manoma da tsarin gwamnati. Majalisar ta kuma umarci Ma’aikatar Noma da samarda Abinci ta haɗa da kafa cibiyoyin bayanai da lura da harkokin noma a kowace yankin siyasa a kasafin 2026.
Kwamitin NEC na wucin gadi kan satar man fetur, ƙarƙashin jagorancin Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya bayyana cigaba da aka samu wajen haɗa kai da manyan masu ruwa da tsaki a masana’antar mai don dakile satar man. Majalisar ta ƙarfafa kwamitin da ya ƙara zage damtse wajen ƙara yawan fitar da danyen mai sama da ganga miliyan 1.72 a kowace rana tare da faɗaɗa aikin sa zuwa kan satar ma’adinai. Ana sa ran Najeriya za ta kai matakin samar da ganga miliyan 2.5 na danyen mai a kowace rana nan da ƙarshen shekarar 2025.
Bello Wakili
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
