Connect with us

Fasaha

Dalibai Makarantun Sakandare A Kwara Sun Karɓi Tallafin Karatu

Published

on

Akalla dalibai marasa galihu 300 da ke makarantun gaba da sakandare daga zababbun al’ummomi a kananan hukumomin Edu/Patigi/Moro na jihar Kwara sun samu tallafin karatu don tallafa musu.

 

Da yake jawabi a wajen taron rabon tallafin karatu da aka gudanar a Ilorin, mai taken “Hatsarori na Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi Tsakanin Dalibai A Manyan Makarantu” wanda Michael Imoudu tare da hadin gwiwar mamba mai wakiltar mazabar Edu/Moro/Patigi na Jihar Kwara, Ahmad Adamu -Saba ya shirya, ya ce za a yi rabon ne kashi biyu.

 

Dan majalisar wanda ya samu wakilcin mai taimaka masa, Muhammed Salihu, ya ce manufar shirin bayar da tallafin shi ne tallafawa daliban da iyayensu ba za su iya biyan wasu kudadensu a makaranta ba.

 

Saba ya bayyana cewa wasu ’yan gata da ke makaranta suma za su iya amfani da kudin wajen siyan littattafansu ko biyan kudin hayar gidansu .

 

Ya shawarci daliban da su tabbatar sun yi amfani da naira dubu dari da ake baiwa kowannen su domin manufar da aka sa a gaba.

 

Saba ta bukace su da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi da sauran munanan dabi’u domin samun ingantacciyar rayuwa.

 

A nasa jawabin mukaddashin Darakta Janar Michael Imoudu National Institute For Labour Studies (MINILS), Fasto Ezekiel Ayorinde, wanda babban jami’in kula da harkokin kasuwanci na Cibiyar, Hassan Surajudeen ya wakilta, ya ce an raba tallafin ne da nufin inganta ilimin daliban.

 

Ya kuma shawarce su da su sanya kudin cikin hikima wajen neman ilimi.

 

A jawabansu daban daban wasu shugabannin al’umma a kananan hukumomin Moro/Edu/Patigi, Muhammed Aliyu Labas da Mohammed Baba (Shonga) sun yabawa mai gudanar da wannan karimcin.

 

Sun bukaci wadanda suka ci gajiyar kudin da su tabbatar sun yi amfani da kudin don manufar da ake son yi.

 

A cikin laccar sa mai taken “Hadarin Shaye-shayen Miyagun Kwayoyi A Tsakanin Dalibai A Manyan Makarantu” Babban Malamin, Abdullahi Galadima ya ce daga bayanan da ake da su matasa na da dabi’ar shiga shaye-shayen miyagun kwayoyi saboda matsin lamba na tsarawa da dai sauransu.

 

Ya shawarci matasa da su guji shaye-shayen miyagun kwayoyi, su kuma yi karatun ta natsu domin kyautata rayuwarsu

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara