Connect with us

Labarai

APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa

Published

on

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Zamfara ta yi kakkausar suka ga gwamna Dauda Lawal kan kalaman da ta bayyana a matsayin bata gari dangane da kokarin gwamnatinsa na magance ‘yan fashi da makami da kuma bayar da tallafi ga wadanda ‘yan fashin suka kashe.

 

Hakan ya biyo bayan wani faifan bidiyo ne da aka ga gwamnan yana magana da manema labarai kan yadda gwamnatinsa ke tafiyar da harkokin tsaro da kuma jin dadin wadanda matsalar tsaro ta shafa.

 

A wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar APC, Yusuf Idris Gusau ya fitar, ya bayyana kalaman gwamnan a matsayin rashin gaskiya da yaudara.

 

Malam Idris Yusuf Gusau ya yi zargin cewa, gwamnatin ta gaza cika wasu muhimman alkawuran yakin neman zabe, musamman alkawarin kawo karshen ‘yan fashi da makami a cikin watanni biyun farko da fara aiki.

 

Sanarwar ta kara da cewa “Gwamna Lawal da alama yana shirin cika shekara biyu a kan karagar mulki ba tare da samun wani ci gaba mai ma’ana ba kan babban alkawarin da ya yi a yakin neman zabe, maimakon a samu ci gaba, matsalar tsaro ta ta’azzara a Zamfara.”

 

A cewar Yusuf Idris, kalaman gwamna Lawal na baya-bayan nan a babban asibitin Gusau sun nuna rashin tausayi da jin kai.

 

“Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnan da yin watsi da wadanda harin ya rutsa da su. “Maimakon ya ziyarci al’ummomin da ‘yan bindiga suka lalata ko aika sahihan tawaga don jajantawa da bayar da goyon baya, Gwamna Lawal ya zabi tafiya daga wata jiha ko kasa zuwa wata, yana jin dadin abokansa da ‘yan uwa yayin da mutanensa ke shan wahala.”

 

Ya yi nuni da cewa, babban abin da ya jawo cece-kuce shi ne ikirarin da gwamnan ya yi na cewa wadanda suka samu raunukan harbin bindiga suna karbar magani kyauta a asibitin kwararru na Yariman Bakura da cibiyar kula da lafiya ta tarayya da ke Gusau.

 

“Wannan karya ce kawai,” in ji Idris. “A makonnin da suka gabata ni da kaina na ga wadanda lamarin ya rutsa da su an mayar da su asibitin Yariman Bakura saboda rashin kudi, abin takaici wasun su sun mutu sakamakon haka, ba tare da taimakon gwamnati ba.”

 

Jam’iyyar APC ta yi kira ga gwamnan da ya fito fili ya bayyana sunaye, al’ummomi, da bayanan kula da wadanda suka ci gajiyar da aka ce sun samu kulawa kyauta, ciki har da kudaden da aka kashe da kuma kudaden da suka dace ko kuma bayanan biyan su.

 

Kakakin jam’iyyar APC ya kuma bukaci Gwamnan da mahukuntan asibitocin biyu da su buga cikakkun bayanai na jinya kyauta da aka yi a karkashin gwamnatinsa.”

 

Jam’iyyar ta kuma bukaci ‘yan jaridan da suka gudanar da hirar da su tabbatar da ikirarin gwamnan tare da zurfafa bincike kan al’amuran da abin ya shafa a lunguna da sako na jihar, kamar karamar hukumar Tsafe, wadanda ba za su iya samun kayan aiki a Gusau ba.

 

REL/AMINU DALHATU.

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara