Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kafa Cibiyoyin Bada Abincin Buda Baki A Manyan Makarantu

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa za ta kafa cibiyoyin bada abincin buda baki a manyan makarantun jihar guda 10, domin tallafa wa dalibai a lokacin azumi.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da al’adu na jihar Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai sakamakon taron majalisar zartaswar jihar da aka gudanar a gidan gwamnati na Dutse.

A cewarsa, gwamnatin jihar na shirin ciyar da mutane sama da miliyan uku da dubu dari takwas a watan Ramadan na bana domin tallafawa gajiyayyu da marasa galihu.

Alhaji Sagir Musa Ahmed ya yi nuni da cewa, gwamnatin jihar ta amince da naira kusan miliyan dubu dari uku domin ciyar a watan Ramadan a cibiyoyi 609 da aka kafa a fadin jihar.

Ya ce shirin tallafin da aka tsara ya yi daidai da manufofin gwamnati na rage wahalhalu ga marasa galihu musamman a wannan lokaci na da ake ciki.

Kwamishinan ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da kafa kwamitin wucin gadi a dukkanin kananan hukumomi 27, wanda kwamishinan kananan hukumomi ko kuma manyan mashawarta na musamman a kananan hukumomin za su jagoranta domin tabbatar da gaskiya.

Sagir Musa ya ce, sauran mambobin kwamitin sun hada da ‘yan majalisar dokokin jihar, mataimaka na musamman, shugabannin kananan hukumomi da DPO na ‘yan sanda.


Sauran sun hada da jami’in tsaro na DSS na karamar hukumar, wakilin hakimai, da sakataren karamar hukuma wanda zai zama sakataren kwamitin.

Hakazalika majalisar ta kuma amince da sama da Naira Biliyan daya da miliyan 125 don ƙarin siyan kayan abinci da za a raba ga marasa galihu, a ƙoƙarin da ake yi na rage wahalhalun rayuwa.

Usman Muhammad Zaria

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Labarai2 hours ago

Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace

Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba...

Labarai3 days ago

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda...

Labarai3 days ago

‘Yan Ƙwadago Sun Yi Watsi Da N48,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

  Ƙungiyar Ƙwadago NLC ta yi fatali da tayin naira 48,000 da Gwamnatin Tarayya ta gabatar a matsayin mafi ƙarancin...

Labarai3 days ago

Tinubu Zai Ciyo Bashin $500m Don Sayen Mitocin Lantarki

  Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ciyo bashin Dala miliyan 500 da nufin samar da mitocin...

Ilimi3 days ago

Za A Fara Daukar Masu Sakamakon Jarabawar NECO A Jami’o’in Birtaniya

  Jami’o’in kasar Birtaniya na shirin fara daukar daliban Najeriya masu shaidar jarabawar kammala sakandare ta NECO. Shugaban hukumar shirya...

Labarai4 days ago

Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki

A yau Laraba 15 ga watan Mayun 2024 ne jirgin Najeriya na farko ya tashi da Alhazan Jihar Kebbi 423...

Labarai4 days ago

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai...

Labarai5 days ago

Tsohon Lauyan Trump Ya Ce Ubangidansa Ya Ba ‘Yar Fina-finan Batsa Toshiyar Baki

Tsohon babban lauyan Donald Trump, Michael Cohen, ya aikata abinda masu gabatar da kara su ka yi ta fatan ya...

Labarai5 days ago

Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya

Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin...

Labarai5 days ago

Jamhuriyar Benin Ta Haramta Fitar Da Masara Zuwa Nijar

Jamhuriyar Benin ta hana fitar da masara zuwa ƙasashen waje a daidai lokacin da farashin hatsi ya yi tashin gwauron...

Mafi Shahara