Labarai
Jirgin Farko Na Alhazan Najeriya Ya Sauka Birnin Kebbi Da Yammacin Asabar
Rukunin farko na alhazan jihar Kebbi, ya sauka filin jirgin saman Ahmadu Bello da ke Birnin Kebbi da yammacin Asabar.
Jirgin mai suna flynas da ya taso daga filin jirgin sama na Sarki Abdul-Aziz da ke Jidda, ya sauka Kebbi ne da misalin karfe 9 da minti 42 na dare tare da alhazai 410 ciki har da jami’an hukumar jin dadin alhazai ta jihar.
Dukkanin mahajjatan suna cikin koshin lafiya sai dai wasu da suke fama da mura sakamakon shan abubuwa masu sanyi davoda da matsanancin zafi da sanyi da tari suka shafa sakamakon shan ruwan sanyi da na’urar sanyaya iska a lokacin da suke kasa mai tsarki.
Kashi na farko da suka isa Najeriya su ne na farko da aka fara jigilar su daga Najeriya zuwa Saudiyya a ranar 15 ga watan Mayun 2024 a yayin kaddamar da jirgin da mataimakin shugaban kasa Kashim Shattima ya yi a Birnin Kebbi, jihar Kebbi.
Abdullahi Tukur
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai16 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
