Connect with us

Labarai

Gobara Ta Hallaka Mutane Arba’in Da Daya A Kuwait

Published

on

Wata gobara da ta tashi a wani gidan ma’aikata da ke garin Mangaf na kasar Kuwait, ta hallaka mutane 41, kamar yadda mataimakin firai ministan kasar Sheikh Fahad Yusuf Saud Al-Sabah ya tabbatar.

Cikin wani jawabi da mataimakin firai ministan ya yi, ya ce gidan matattara ce ta mutane da ke kananan ayyuka a kasar, wanda mafi akasarin su bakaken fata ne.

Sheikh Al-Sabah ya alakanta tashin gobarar da tsantsar son zuciya da kuma rashin bin ka’ida da wasu dillalan  da ke bada gidajen haya ke nunawa.

Bayanai sun ce wutar ta tashi da misalin karfe 6 na safiyar Laraba agogon kasar, kamar yadda Manjo Janar Eid Rasheed Hamad daya daga cikin mahukuntan kasar ya tabbatar.

Ya ce an yin nasarar ceto wasu da dama, yayin da wasu suka gamu da munanan raunuka, sai dai kuma abin tashin hankalin shi ne yadda wutar ta kona mutane 41 kurmus.

Manjo janar Rasheed ya ce kowanne lokaci hukuma na iya bakin kokarinta wajen ganin ta rage cinkoso a irin wadannan gidaje, amma masu bada haya sai su yi amfani da barauniyar hanya wajen tara mutane kawai don neman kudi.

Har yanzu dai babu cikakken bayani kan musabbabin tashin gobarar sai dai jami’ai na ci gaba da bincike.

 

Labarai

Labarai13 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara