Labarai
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano Ta Yi Wawan Kamu
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama wasu mutane 19 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane da sauran laifukan da suka shafi ‘yan fashi.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Sufurtandan Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Kano.
Ya ce an samu nasarar kame mutanen ne ta hanyar sintiri da kuma tattara bayanan sirri.
Kiyawa ya bayyana cewa, kayyakin da aka gano sun hada da bindigogi kirar AK-47 guda biyu, bindigarsamfurin harbi ka ruga daya, bindiga kirar famfo guda daya, alburusai 26, harsashi masu rai guda 17, motoci guda biyu, raguna 16, da sauran muggan makamai da na fasa gidaje.
“Ana ci gaba da bincike kuma nan ba da jimawa ba za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu.”
Ya yi nuni da cewa Kwamishinan ‘yan sanda, CP Mohammed Usaini Gumel, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da yin aiki tukuru domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi da kuma gurfanar da masu aikata laifuka a gaban kuliya.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai7 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai16 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
