Connect with us

Labarai

Za a Dauki Mataki Kan Masu Cin Zarafin Yan Aikin Gida

Published

on

A wani mataki na kare hakkin ‘yan aikin gida da ma kare iyayen gidan da ake yi wa aikin daga fuskantar wata matsala daga kowanne bangare, majalisar dattawan Najeriya ta ce akwai bukatar samar da hukumar da zata rika tattara bayanan ‘yan aikin da kuma iyayen gidan na su.

Majalisar ta ce za a samar da hukumar ne domin tabbatar da kare ‘yan aiki wadanda a ko da yaushe suke fuskantar cin zarafi daga wajen iyayen gidansu.

Sannan kuma a kare iyayen gidan da a wasu lokutan ke fuskantar hadari daga masu yi musu aikin.

Matakin samar da hukumar da majalisar ke shirin yi ya biyo bayan wani kuduri da daya daga cikin ‘yan majalisar sanata Babangida Hussaini, ya gabatar a zauren majalisar wanda kuma ya samu cikakken goyon baya da kuma tsallake karatu na biyu a majalisar.

Sanata Babangida Hussaini, ya ce rashin dokar da zata rinka sanya ido da kuma bibiyar irin wadannan al’amura da ma sanya ido a kansu ya sa cin zarafi ‘yan aiki ya yawaita a Najeriya.

Sanatan ya ce irin hakan kuma kan janyo faruwar manyan laifuka kamar kisan kai a tsakanin ‘yan aiki da iyayen gidansu.

Babangida Hussaini ya ce,” A wasu lokuta zaka ga ba a biyan ‘yan aiki hakkinsu kamar yadda ya kamata, wadansu ana cin mutuncinsu inda wadansu ma har rasa rayukansu suke.”

Ya ce,” A bangaren masu daukar ‘yan aikin gidan kuma wato iyayen gida ke nan ana samun matsaloli kamar hada kai da masu aikin gida da wasu bata gari wajen sace sace ko kuma wani lokacinma a lalata yaran gida.”

” Wannan duk ya biyo bayan rashin tsari da ma sanya idanu ne.” in ji shi.

Kudurin dokar samar da hukumar dai zai gindaya wasu sharuda da sai an cika su kafin a dauki ‘yar aiki ko dan aiki, sannan dole shi ma mai daukar ‘yan aikin a samu bayanansa.

Sanata Babangida Hussaini, ya ce idan wannan kudurin ya zama doka to akwai dokar da za ayi wadda iyayen gida ba za su rinka cin mutuncin ‘yan aiki ba, sannan wajibi ne kuma a rinka kula da ci da sha da wajen kwanan ‘yan aiki.

Bashir M

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara